#dubunity
Explore tagged Tumblr posts
Text
V
De la Barre des navres à Celle Dubunal. Le Skiper Kévin Escoffier, Récament Placé en Garda à vue pour des aggions sexelles Qu’il Conteste, est attendance will Lundi au tribunal correctionnel de Paris, Où il pursuit le canard enchaîné pour diffamation. En Cause, Un artist de Fin Octobre 2023 Titré «#metoo de la voile: la fédé tire des bords’, évoquant la proCédure disciplinaire décleché pair la…
0 notes
Photo

Energy Of Dub – CZ&SK Dub Unity Compilation Vol 1 – Une union Dub sans faille de la République Tchèque et de la Slovaquie ! = https://culturedub.com/blog/energy-of-dub-czsk-dub-unity-compilation-vol-1/ = #dub #stepper #steppa #soundsystem #czech #cz #sk #slovakia #prague #bratislava #compilation #culture #music #noprofit #unity #dubunity #chronique #review #culturedub @energyofdub @echoboy_dub @steppers_division @jujuplanetdub @tropicaldubconnection @culturedub https://www.instagram.com/p/Ci2BuaVsUX4/?igshid=NGJjMDIxMWI=
#dub#stepper#steppa#soundsystem#czech#cz#sk#slovakia#prague#bratislava#compilation#culture#music#noprofit#unity#dubunity#chronique#review#culturedub
2 notes
·
View notes
Photo

AL'UMMAR GARIN GASHUA, BA ZASU TABA MANTAWA DA IRIN WANNAN RANAR BA. Yadda idan watan Azumi ya kama, al'umma kan fito suna nunayya zuwa sararin samaniya da yatsunsu, fusaku cike da farin ciki, hakanan dandazon dubun-dubatan al'umma suka fito bakin titi tsawon Kilometer 7, tun daga masauki har zuwa Masallacin Central Mosque Gashua, suna masu murna da shewar shaida ganinsa. Saukarsa cikin Masallaci nutsuwa ya kwacewa dandazon ayarin mahalarta, domin kowa ya shiga hali na shauki matsananci da ganinsa, mai gabatarwa yayi ta magana akan a saurara amma abin sai ya cutura. Ko da wannan Dan Baiwa Jikan Waliyyin ALLAH ya amshi abin magana, ya furta wasu kalmomi ababen takaitawa, kai kace daukewar ruwan sama, haka kowa ya dawo hayyacinsa. LALLAI WANNAN RANA, RANACE TA TARIHI A GAREMU, DOMIN AL'UMMAR GASHUA SUN NUNA TSANTSAR SOYAYYA GA WANNAN HAZIKIN DAN BAIWA, KUMA MUN DAUKI DUKKAN SAURAN RANAKU CIKIN KEWARSA. Muna kara Jaddada godiya ga Halarar Khalifa da ya samu damar zuwa garinmu, muka amfanu sosai cikin kimtsattsun bayanansa. (Muhammad Usman Gashua✍️) ALLAH YA KARA LAFIYA, KARIYA DA AMINCI. ALHAMDULILLAH. https://www.instagram.com/p/Cn7p_HVo68a/?igshid=NGJjMDIxMWI=
0 notes
Text
Taron Jam'iyyar PDP Na Kaduna: 'Yan Najeriya Sun Kosa Da Jagorancin APC!
Taron Jam’iyyar PDP Na Kaduna: ‘Yan Najeriya Sun Kosa Da Jagorancin APC!
Daga Bello Ahmadu Alkammawa Babban Birnin Kaduna a yau Litinin 17/10/2022 ya tsaya chak saboda yadda dubun dubatan mutane suka rika tururuwa zuwa wajen taron Jam’iyyar PDP na Kasa da aka gudanar a filin wassanin da ake kira (Ranchers Bees) a Turance. Ciki da waje duka mutane ne iyakar ganinka, hasalima birnin ya dauki baki a ko’ina cike da farinciki da annashuwa tamkar wani kasaitaccen bukin…

View On WordPress
0 notes
Text
MU GANI A KASA Hot love story page 1 and 2
MU GANI A KASA Hot love story page 1 and 2
MU GANI A KASA Hot love story page 1 and 2 GAWURTATTU BIYAR.🔥 Page 1-2 Godiya ga Allah (S A T) da ya sake bani dama da iko da sake zaman rubuta muku wannan labarin, dubun tsira da aminci su ƙara tabbata ga manzonmu Annabi Muhammad (S A W). Da fatan zaku bini sannu a hankali domin jin inda wannan karon labarina ya nufa. Haƙƙin mallaka na Ummu Affan ne, ban yadda a juya mini labari ta ko wacce…

View On WordPress
0 notes
Text
DALILIN DA YASA MAI NAIRA YA ZAMANTO GA GARA GASA,KUMA MAI DUBUN MASOYA A FADIN JIHAR ZAMFARA
*MEDIA ADVERTS**Media/News Campany Nigeria Limited.**DALILIN DA YASA MAI NAIRA YA ZAMANTO GA GARA GASA,KUMA MAI DUBUN MASOYA A FADIN JIHAR ZAMFARA**Cikin Masu fada a ji na fadin jihar Zamfara Mai Naira (S•A) ya zamanto cikin jerin mutanen farko saboda irin mu’amalarsa da mutane karkashin Jagorancin mai Girma Gwamnan jihar Zamfara.**A wata Ganawa Da Jagororin Kungiyar Mai Naira foundation Da suka…

View On WordPress
0 notes
Text
GAME DA FITAR SHAIKH ZAKZAKY WAJE JINYA: ZUWA GA GWAMNATIN NIJERIYA!!

Bisa ga furucin babban Lauyan gwamnatin Kaduna da ke kare muradun gwamnatin a shari'arta da Shaikh Zakzaky Bayero Dari, da kuma abin da ya bayyana a zantukan mai magana da yawun shugaban kasa Garba Shehu: Wai gwamnatin Nijeriya ba ta so a ba Shaikh Zakzaky damar zuwa jinya kasar waje ne (duk da matsanancin halin da yake ciki), saboda wai IN YA FITA WAJE BA ZAI DAWO A CI GABA DA YI MASA SHARI'A KAN LAIFUFFUKAN DA AKE TUHUMARSA DA SU BA!! Wannan ikirari na wakilan gwamnati da ban mamaki yake ga duk wanda ke rayuwa da Shaikh Zakzaky (H) a duniya daya, kuma a zamani daya. Da gaske ne wannan gwamnatin ta dan kama karya Buhari, tana kauda kanta kan hakikanin al'amura ne da gangan kawai don cimma munanan kudurorinta, musamman kashe Shaikh Zakzaky (H) da share almajiransa daga samuwa. In banda haka, waye a duniyar nan ya Shaidi Shaikh Zakzaky da tsoro??? Wa ya shaide shi da karya ko saba alkawari??? Ku binciki tsaffin Fayelolinku na ofisoshin 'yan sandanku ku gani, za ku ga cewa;- Tsare Shaikh Zakzaky da aka yi a shekarar 1981 a Sakkwato, ba zuwa aka yi aka kama shi ba, almajiransa aka kama, da ya ji labari sai ya kai kansa ga 'yan Sanda, ya ce shi ma ya aikata irin laifin da daliban nasa suka aikata, ko dai a sake su duka, ko kuma a hada da shi a tsare su duka!! Shi ne aka tsare shi tsawon shekaru 3. A tsarewar da Abacha ya yi masa a 1996, duk da cewa jami'an tsaro sun je gidansa, amma sun ce masa ne ana bukatar ya je ofishinsu a Kaduna ya amsa wasu 'yan tambayoyi, sai ya ce ya san kama shi za su yi, Amma a je din! Shi ya sa ma ya tafi a motarsa tare da rakiyar kaninsa da almajiransa daya. Shi ma aka tsare shi fiye da shekaru 3. A lokacin mulkin Babangida a shekarar 1992, da jami'an tsaro suka addabi jama'ar Katsina da kisa da hauka, da sunan wai suna neman almajiran Shaikh Zakzaky, sai Shaikh din ya bada sanarwa a gidan rediyon BBC cewa, duk wani almajirinsa da ke garin Katsina, ya kai kansa ofishin 'yan Sanda mafi kusa da shi, su yi masa duk abin da za su yi!! A haka daruruwan almajiransa suka mika kansu ga 'yan sanda cikin izza!! A lokacin mulkin kama karya na Sani Abacha, an yankewa manya kuma fitattun almajiran Shaikh Zakzaky guda biyar hukuncin kisa da zarar an kama su ba tare da kaiwa kotu ba, dukkanin wadannan mutane 5 sun buya an kasa kama su. Shaikh Zakzaky ya aiko masu da umarni cewa duk su kai kansu ga jami'an tsaro, in ya so su yi masu duk abin da za su yi! Shaikh Yaqubu Yahya ya kai kansa hedikwatar 'yan sanda a Katsina, Shaikh Mukhtar Sahabi ya Mika kansa a Kaduna, Shaikh Qasim Umar ya Mika kansa a Sakkwato, sauran ma duk suka je ga jami'an tsaro suka ce ga mu ku yi yadda ku yi!! A wannan ta'addanci na Buhari wanda Burtai ya jagoranta a 2015 a Zariya, an tsara yadda za a tseratar da Shaikh tun a daren Asabar, da aka ce ya fito a tseratar da shi, ya ce har abada ba zai gujewa kazamai irin sojojin Nijeriya don kawai suna da Bindiga ba!! Iya abin da za su iya shi ne kisa, to su zo su same shi a cikin gidansa su kashe! Amma ya fi karfin yi masu gudu!! A jawabinsa na cikar Da'awarsa shekaru 25, ya fada a gaban dubun dubatar mutane cewa, Ko Janaral aka ce masa Zakzaky zai gudu, zai ce karya ne!!! Ba Zakzaky ba, hatta dan karamin almajirinsa Shaikh Mustapha Lawan Potiskum, yana zaune a cikin masallaci sojoji suka zo kashe shi, suka bude masa wuta amma ko dukawa da nufin ya kauce bai yi ba, da yake jawabi a masallacin Juma'a ya ce masu; Billahil'Azeem na fi karfin in kwantawa harsashinku!! Duk wadannan abubuwa da na jero ku shaida ne a kansu, kuma kun san Zakzaky ba ya tsoronku! Kun fi kowa sanin cewa ba ya karya ba ya yaudara bare karya alkawari. To, tunda duk kun san da wannan, me zai hana ku same shi a inda kuke tsare da shi, ku ce masa; Ba ma so mu bari ka je waje ne don muna ganin ka gudu kenan ba za ka dawo mu hukuntaka ba, amma yanzu muna so ka mana alkawarin za ka dawo, don mun yarda ba ka karya bare saba alkawari!! To na rantse da Ubangijin da ya halicci duniya da abinda ke cikinta, in ya amsa muku cewa zai dawo kwana daya bayan warkewarsa, to ko awa daya ba zai kara ba!! Kuma ba wanda zai iya hana shi dawowa!! Mafi kololuwar abin da za ku iya yi fa shi ne kisa! Shi kuma mafi kololuwar burinsa kenan!! In har da gaske tsoron kar ya ki dawowa ne hujjarku ta rashin ba shi damar zuwa ganin likita, to ku gwada wannan ku gani, in kuma ba ku yi haka ba, to karya kuke yi! Ba dalilin kin dawowarsa ya sa kuka ki ba shi Beli ba, mummunan kudurinku ku ke son zartarwa, shi kuma wannan a hannun Allah yake ba a hannunku ba!! -Adamun Adamawa
from Blogger https://ift.tt/2YX5a24
0 notes
Photo

Tu #Bhikari samhaj raha hai mjhe !#Kaasa paltun tw teri #Kainat le #Dubun🚬
0 notes
Text
Sabuwar Wakar Kawu Dan Sarki Lokaci Audio Mp3.
Lokaci by kawu Dan Sarki 2023 Audio Mp3. Daukaka nufin Allah haka shahara kudirar Allah tabbas dukkansu suna samuwa ne daga mai sama Allah sarki mahaliccin duniya da lahira baki daya, babu shakka masu shahara da masu daukaka wasu na dauka duk abu daya ne amma kuma akwai banbanci dauka lokacici ita kuma shara da imance cewar masu hasashe da yaran Hausa. Bayan dubun gaisuwa da kuma shiga cikin…

View On WordPress
0 notes
Text
Mahaifi ya yi wa yar sa fyade har tayi ciki
Dubun mahaifin ta cika ne bayan yarinyar ta kai kokenta wajen kungiyar kare hakkin mata da yara ta FIDA, wadda ta sanar da ‘yan sanda.
0 notes
Text
Hotuna: Yanda Aka kama magidanci Turmi da tabarya danne da matar makwabcinsa
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Dubun wani magidanci dake lalata da matar makwabcinsa ta cika yayin da aka kamashi turmi da tabarya akan matar makwabcin nasa a Otal kuma aka daukesu hotuna dan tabbatar da faruwar Lamarin.
cigaba da karatu » from Hutudole: labarai da hausa https://ift.tt/2S9LSWa via https://ift.tt/2whmJRK
0 notes
Text
Masarautar Dass Ta Tsaya Chak, Saboda Gimbiyar Zazzau!
Daga Bello Ahmadu Alkammawa MASARAUTAR DASS dake cikin Jihar Bauchi ta karbi bakuncin dubun dubatan mutane wadanda suka yiwa birnin tsinke domin halatar bukin nadin Gimbiya Bilkisu Shiba Zailani a matsayin Jagaban Matan Dass ta farko wanda Mai Martaba Sarkin Dass Alhaji Usman Bilyaminu Usman ya yi a fadarsa ranar 10/09/2022. Mako daya kafin ranar bukin, birnin na Dass ya soma karbar bakuncin…

View On WordPress
0 notes
Text
Hoto: Kalli Malamin dake yin luwadi da almajiransa, kuma yana bada hayarsu a Sakkwato
New Post has been published on https://is.gd/TYx7T8
Hoto: Kalli Malamin dake yin luwadi da almajiransa, kuma yana bada hayarsu a Sakkwato
Ke duniya ina zaki damu ne, yayin da ake zaton wuta a mekara sai gata an tsinceta a masaka, anan dubun wani Malamin makarantar allo ne ta cika bayan kamashi da laifin yi ma kananan yara almajirai fyade irin na luwadi, inji rahoton jaridar Daily Nigerian.
Majiyar Legit ta ruwaito dalibai da dama na makarantar allon dake unguwar Arkilla a cikin garin Sakkwato sun tabbatar da cewa malaminsu mai suna Murtala Muade ya sha yi musu fyade, haka zalika sun ce yana bayar da hayarsu ga yan luwadi suna amfani dasu.
Ke duniya! Kalli Malamin dake yin luwadi da almajiransa, kuma yana bada hayarsu a Sakkwato
Maude Source: Facebook
Malam Maude ya amince da wannan zargi, sai dai yace shi yasan yara uku kacal ya taba yi ma fyade, amma an samu wasu almajirai uku da suka bayyana kansu, inda suka ce suma yana musu fyade, wanda hakan ya kawo adadin daliban da malamin yake zakke mawa zuwa shida.
Kwamishinan Yansandan jahar Sakkwato, Ibrahim Kaoje ya bayyana cewa a ranar 22 ga watan Maris ne wani lauya dake aiki da hukumar kare hakkin biladama ta kasa, Hamza Liman ya kai karar malamin zuwa ofishin DPO na Yansandan Arkilla, daga nan aka mika maganar zuwa shelkwatar Yansanda.
Kwamishinan yace duka duka shekarun yaran bai haura 4 zuwa 15 ba, kuma yawancinsu yan Zamfara ne, amma Malamin ya mayar dasu abin huce sha’awarsa, har ma yana bayar dasu haya tamkar karuwai, don haka kwamishina Kaoje ya gargadi iyaye dasu daina kai yaransu almajiranci nesa da gida.
Amma abinka da ja’irin Malami, yayin da yake ganawa da manema labaru, sai ya kada baki yace kaddara ce, dama can Allah Ya kaddara sai yayi ma almajiran nasa fyade.
Zuwa yanzu dai an garkame wannan makarantar allo, kuma Yansanda sun kaddamar da bincike akan wannan lamari mai muni, sa’annan an mika almajirai shidan zuwa ga gidauniyar ceton yara, yayin da kungiyar lauyoyi Musulmai suka dauki nauyin ciyar dasu.
0 notes
Text
dubunism / Soldefvski
RT @twicett520: *while Samo were flirting* Tzuyu: The ambiance here is nice! Nayeon: It’s romantic! Chaeyoung: Honey, want to marry me? *sl…
View On WordPress
0 notes
Quote
Daga Littafin "Muhimman Raneku 400 A Tarihin Harkar Musulunci"—Na Cibiyar Wallafa da yada ayyukan Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)RANA TA 76:*12 September, 1996 (29 Rabius Thani, 1417H):*A wannan ranar aka fara wakiar Abacha, wacce ta fara a Asubahin wannan ranar Alhamis 12/9/1996, da zuwan cincirindon yan sanda shake da motoci, dauke da akwatunan harsasai zuwa gidan Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky don su kama shi.A rannan, mataimakin kwamishinan yan sanda na Kaduna, Muktar Ibrahim, shine ya jagoranci harin, wanda a lokacin da suka zo gidan Malam Zakzaky, sun nuna masa takardar izini (warrant) a kan za su yi binciken makamai ne a gidan nasa. Bayan ya basu damar binciken, suka shiga suka bincika ba su samu ko tsinke da sunan makami ba, sai kuma ya nemi cewa za su tafi da Shaikh din, don ya je ofishinsu a Kaduna ya sa hannu akan cewa ba a samu makami a gidansa ba.Shaikh Zakzaky yace masa ni ba yaro bane, kace min kun zo ku kama ni kawai. Don haka ya aminta musu akan su tafin. Malam ya zabi cewa tunda sun ce ba kama shi suka yi ba, to zai tafi a cikin motarsa ce, Malam Muhammad Turi zai tuka shi, kuma kaninsa Malam Badamasi Yaqoub zai raka shi.Ashe a daidai lokacin da suke gidan Shaikh Zakzaky, wasu yan sandan sun riga sun je gidan Alhaji Hamid Danlami, wanda shine Manajan jaridar Almizan, sun kama shi tare da maaikacin jaridar mai suna Abubakar Abdullahi Almizan, sannan kuma sun kama wani mutum mai suna Malam Shittu, wanda aka aiko shi daga shagon aikinsu na Printing don ya kawo Almizan din satin da aka riga aka buga.Sai da aka je gab da shiga Kaduna, suka roki Shaikh Zakzaky kan ya koma cikin daya daga cikin motocinsu, ya fita daga tasa motar don kar a shiga gari a iya gane cewa an kamo shi ne. Bayan da ya amsa musu, aka bude masa mota sai ya ga wadannan mutum ukun da aka kamo su a ciki.Da aka je hedikwatan yan sandan kwantar da tarzoma (Mopol) a Kaduna, sai suka bayyana aniyarsu na tsare Malam Zakzaky da wadannan mutum uku din, kuma suka sallami Malam Turi da Malam Badamasi a kan su koma gida su ba a da bukatarsu a lokacin.Wakiar Abacha ta gudana ne baki daya bisa umurnin shugaban kasa na mulkin soja a lokacin, Janaral Sani Abacha. Ta hannun gwamnansa na Kaduna, Hamidu Ali, tare da gudummawar kwamishinan yan sanda na lokacin Yakubu Shuaibu.RANA TA 77;*13 September, 1996 (1 Jimadal Ula 1417H):*A ranar Juma'a 13/9/1996 ne dubun-dubatan yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky suka hadu a Zariya, inda suka gabatar da Muzaharar Allah-wadai da kamun Jagora, Shaikh Ibraheem Zakzaky da gwamnatin Abacha ta yi. Ko da yake Muzaharar ta gudana ne a duk fadin kasar, amma ta Zariya ta musamman ce.Muzaharar ta faro ne daga masallacin Jumaa na sabon garin Zariya, isowar goshinta kofar Doka ke da wuya, yan uwa suka gamu da jamian yan sandan kwantar da tarzoma a daidai shatale-talen hanyar Jos dauke da muggan makamai, inda suka budewa yan uwa wuta da tiyagas da harsasai masu rai. Nan take aka samu Shahidai 15, da taimakon Allah yan uwa suka dake da Kabbara da Hailala da jefa duwatsu har sai da suka kora yan sandan nan suka gudu da kafafunsu suka bar tankan yakinsu. Sannan Muzahara ta cigaba da gudana har zuwa muhallin da aka tsara za a rufe ta, wato Babban Dodo a cikin garin Zaria. Tsayuwar wanda ke Jagorantar yan uwa a lokacin, Malam Muhammad Turi, da ya zama bai gudu ba duk da ruwan wutan da ake yi, ya taimaka sosai wajen dakewar yan uwa da rashin tarwatsewarsu. A yammacin wannan ranar ne kuma Shaikh Muhammad Turi ya jagoranci janazar Shahidan, wanda aka bizne su duk a garin Zariya.RANA TA 78;*14 September, 1996 (2 Jimadal Ula 1417H):*A ranar Asabar, washe-garin wakiar kofar Doka da duddukun asubahi, jamian tsaro suka je inda suke tsare da su Shaikh Ibraheem Zakzaky da almajiransa uku, suka dauke su daga ofishin na mopol da ke Kaduna cikin motoci biyu, aka kama hanyar Kudancin kasa da su don tsarewa. A rannan suka kai Jagora, Shaikh Zakzaky kurkukun Fatakwal (Port Harcourt) babban birnin jihar River. Alhaji Hamid Danlami aka kai shi Kurkukun Enugu. Malam Abubakar Almizan kuma aka kai shi kurkukun Calabar ta jihar Rivers, sai Malam Shittu aka kai shi kurkukun Benin ta jihar Edo. Tun da aka kai su aka tsare a wannan ranar 14 ga Satumbar 1996 din, sai a ranar 2/6/1997, bayan sun shafe kimanin watanni tara a tsare, sanna aka maido da su Kaduna don yi musu sharia.RANA TA 79;*18 September, 1996 (6 Jimadal Ula,1417H):*A ranar Laraba 18/9/1996, yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky suka kuma fitowa a garin Kaduna don yin Muzaharar jaddada kira a saki jagoransu daga kamun da Abacha ya yi masa a ranar 12/9/1996. Tare da bayyanawa duniya irin taaddancin da jamian yan sanda suka yi na kashe mutane a ranar 13/9/1996 a Zariya. A wannan ranar duk da barazanar kwamishinan yan sandan Kaduna, Yakubu Shuaibu da yace duk wanda ya fito Muzahara a ranar zai karya masa kafa, yan uwa sun fito Muzaharar wacce aka faro ta daga Masallacin Maiduguri road a cikin garin Kaduna. Sai dai a wannan ranar yan sanda sun sake yin taaddancin, inda suka bude wuta a kan yan uwa masu Muzaharar da harsasai masu rai, an tabbatar da yan uwa guda shida sun samu shahada a wannan Larabar, sai dai ana tunanin sun fi haka, saboda akwai wadanda yan sanda suka kashe suka kira wani Malami mai suna Abubakar Tureta wanda makiyin Harka ne suka sa ya yi musu sallah da bizne su a makabarta. Sannan sun kama yan uwa da dama a rannan, ana zargin sun harbe wasu. RANA TA 80;*20 September, 1996 (8 Jimadal Ula, 1417H)*A ranar Jumaa 20/9/1996, kamar yan kwanaki bayan kama Shaikh Zakzaky da bude wuta a kan almajiransa da jamian tsaron Abacha suka yi, sai kawai ya zama wakia ta cigaba a duk kasar, inda ba kawai yan sand aba, har ma yan tauri hukuma ta rika amfani da su don afkawa yan uwa. A wannan ranar ne yan tauri suka kashe Shahid Usman Kassu a garin Goronyo ta jihar Sokoto.Wani dan tauri mai suna Abu A.D ya dabawa Shahid Usman wuka a cikin masallacin Jumaa na garin, a yayin da ake waazi kafin sallar Jumaa. An tabbatar da cewa yan taurin sun kai wannan harin ne da umurnin shugaban karamar hukumar Goronyo na lokacin, Abdullahi Dankura. A wannan Jumaar ne har ila yau kansilar garin Yar Rimawa ta jihar Sokoto, Shehu Dan tsamaye, tare da hadin guiwar hakimin garin da shugaban karamar hukumar (wancan Audu Dankura din) da sarkin gabas na karamar hukumar Goronyo, Sambo Usman, suka nemi kwamishinan yan sanda na jihar Sokoto a lokacin, Gimba Umar, ya turo musu da mota uku na yan sanda zuwa garin, Kansila Shehu Dantsamaye ya kai yan sandan masallaci ya rika bi sahu-sahu yana tsamo yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky yana nuna musu suna harbewa da bindiga. Cikin wadanda suka harbe har lahira a wannan ranar akwai wakilin yan uwa na garin, Malam Ibrahim Idris, da kaninsa da suke uwa daya, Umar Ilyasu. Sannan Dantsamaye ya je da yan sanda har sashen mata na masallacin, ya nuna musu mahaifiyar su Malam Ibrahim da Umar, dattijuwa yar shekaru 62 mai suna Aliyatu Rabiu suka harbeta.— Ba da jimawa ba littafin zai kammalu da izinin Allah.
http://www.5five-stars.com.ng/2020/03/wasu-raneku-biyar-5.html
0 notes
Text
Sabuwar Wakar Nura M Inuwa Rana Dubu Video.
Sabuwar Wakar Nura M Inuwa Rana Dubu Video.
Tafi zuwa kasa Dan kallon video din Rana Dubu sabuwar Wakar Nura video. Sabuwar Wakar Nura M Inuwa Rana Dubu wan Nan wata sabuwar wakace Mai dadin gaske da shahararren wakin Nan Nura m Inuwa ya saki domin faranta ranku masoya Nura ya bayyana farin cikinsa da kauna agareku masoya Baki daya. Nura ya Kara da cewa Yana Mai bawa dubun masoya hakuri bisa jinkiri na rashin jin wakokinsa akan lokaci Haka…

View On WordPress
0 notes