Tumgik
#Mahanga bay
wvlfcvlt-blog · 8 years
Photo
Tumblr media
Hello, love.
7 notes · View notes
photographybyamelia · 3 years
Text
Tumblr media
📷 2021, Mahanga Bay
0 notes
rebgarof · 5 years
Link
Marlon always with the waiata in times of grief. I think “Purea Nei” has to do with purifying? Next lullaby to learn. “Henare Mahanga rāua ko Hirini Melbourne waiata in Le Bons Bay church before the War #songsofcomfort”
Purea nei e te hau Horoia e te ua Whitiwhitia e te ra Mahea ake nga poraruraru Makere ana nga here.
E rere wairua, e rere Ki nga ao o te rangi Whitiwhitia e te ra Mahea ake nga poraruraru Makere ana nga here, Makere ana nga here.
////
Scattered by the wind washed by the rain and transformed by the sun, all doubts are swept away all restrains are cast down. Fly O free spirit, fly to the clouds in the heavens, transformed by the sun, with all doubts swept away and all restrains cast down. Yes, all restrains are cast down.
(Another version from Anna Coddington.)
0 notes
isiyasy · 5 years
Text
DALILAN YUNKURIN IMAM HUSAINI (A.S)
Hakika Imam Husaini (a.s) bai boye dalilin fitarsa daga birnin Madina da kuma dalilan da suka sa ya shirya yakan Yazid ba. Ya riga da ya ba da gamsasshiyar amsa ga wadanda suke so su sani. Ya bayyana manufar wannan yunkuri nasa, da kuma tafarkin da zai bi wajen yakan wannan sabuwar gwamnati ta Umayyawa. Dukkan wadannan abubuwa dai suna cikin wasikar da ya aika wa kaninsa Muhammad bn Hanafiyyah, inda ya bayyana cewa, lalacewar yanayin siyasa, zamantakewa da akidun al'umma, bugu da kari kan nauyin da ke kansa na gyaran al'umma, su ne suka sanya shi barin Madina da kuma jagorantar wannan babban yunkuri na fada da mulkin zaluncin Umayyawa. Wannan wasika ta sa tana nan kamar haka: "Ni ban fito domin girman kai ko alfahari ba, ba kuma domin barna a bayan kasa ko zalunci ba. Abin da kawai ya fito da ni shi ne neman gyara a cikin al'ummar kakana, Manzon Allah (s.a.w.a.). Ina nufin yin umurni da kyakkyawan aiki da hana mummuna, in kuma bi irin rayuwar kakana da babana.....(1)". Daga nan kuma sai ya yi bayanin dalilin da ya sa yaki yarda ya yi mubaya'a wa Yazid, da cewa: "Yazid dai lalatacce ne, mashayin giya, mai kashe rayukan da Allah Ya haramta, baya ga haka kuma yana bayyana wadannan munanan ayyuka nasa a fili. Don haka mutum kama ta ba zai taba yin bai'a wa mutum kamar Yazid ba(2)". Hakika shari'an Musulunci ya shar'anta cewa dole duk wani shugaban da zai jagoranci al'umma ya kasance yana kula da ka'idar adalci da kuma rashin nuna bambanci. Dole ne ya ba riki shari'ar Musulunci da kuma bukatun al'umma sama da komai, ba ya halalta ya yi sako-sako da dokokin Allah. Dole ne ya nesanci zalunci da kuma yin amfani da matsayinsa wajen tara kudi, jin dadi da kuma wulakanta mutane, ko kuma fifita na kusa da shi ko kuma danginsa. Sanannen abu ga Imam Husaini (as.) da kuma sauran al'umma cewa Yazid mutum ne da bai cancanci ya shugabanci al'umma ba, don kuwa mutum wanda babban burinsa shi ne yada fasadi a bayan kasa da kuma zaluntar bayin Allah. Yazid mutum ne da ya nitse cikin sabon Allah da suka da neman mata, shan giya wasa da birrai da dai duk sauran nau'o'i na wargi da wasa. Baya ga haka kuma sanannen abu ne cewa dukkan al'umma sun yarda da cewa bai kamata a ba da shugabanci ga mutumin da ya rasa siffa wacce za ta kasance abin koyi ga al'umma ba cikin ayyuka da mu'amalolinsa, sannan kuma dole ne ya kasance mutum masanin siyasa da zamani. To idan duk mun fahimci haka, to ya ya za mu yi tsammanin mutum kamar Imam Husaini (a.s) - wanda ya kasance jika ya ke wa Manzon Allah (s) kana kuma dan Fatima da Aliyu (a.s), sannan kuma burin dukkan al'umman musulmi - zai mika kai ga wannan fajiri Yazid dan Mu'awiyyah. To saboda wadannan dalilai ne ya sa Imam Husaini (a.s) ya ki ya yi bai'a wa Yazid, kuma ma ya dau makami don yakansa, kamar yadda ya bayyana wa mabiyansa a duk inda ya yada zango don su fahimci matsayarsa ta siyasa da kuma irin halin da ake ciki. A cikin wasikarsa ga mutanen Kufa, Imam Husaini (a.s) ya bayyana musu siffofin shugaba na kwarai, don ya wayar musu da kai da kuma bayyana musu wane ne ya cancanci ya zamanto shugaba. A cikin wasikar ya bayyana musu cewa: "...Na rantse, shugaba shi ne wanda ya yi shari'a da Littafin Allah, wanda ya ke gudanar da gaskiya da kuma adalci, wanda kuma yake bayyanar da hakikanin addinin gaskiya, sannan kuma wanda ya ba da kansa don Allah(3)". Haka nan kuma ya rubuta wa manyan shuwagabanni Basrah; wato Malik bn Mas'ma' al-Bukra, Al-Ahnaf bn Kais, al-Manzar bn al-Jarud, Mas'ud bn Amru, Kais bn Haitham da Amru bn Ubaid bn Mu'ammar wasika inda ya ke cewa: "...Ina kiranku zuwa ga kiyaye Littafin Allah da Sunna ManzonSa (s) da kuma aiki da su. A halin yanzu an ajiye Sunnar Annabi (s) a gefe kana kuma an raya bidi'a. Matukar kuka riki wannan kalami nawa, to ni kuwa zan ja ku zuwa ga hanya madaidaiciya. Amincin Allah ya tabbata a gare ku(4)". Hakika Imam Husaini (a.s) yana dubin gwamnati, siyasa, al'umma da kuma shugabanci ne a bisa mahanga ta Alkur'ani mai girma. To amma shi Yazid, sabanin haka, yana dubin wadannan al'amurra ne a bisa mahangar zalunci da babakere. Shugabanci, a wajen Imam Husaini (a.s), kamar wata mota ce wacce za a sanya mutane a kan tafarki shiriya da kuma isa zuwa ga hallarar Ubangiji, tafarki ne da sanya mutane a kan dokokin sama don su gina rayuwarsu akan tafarkin gasikya da kuma kyawawan dabi'u. A fahimtarsa, gwamnatin Musulunci tana karkashin kulawa ne na Musulunci da dokokinsa, wanda ita ta hakan ne za ta tsara nata dokoki da kuma ka'idoji. Haka nan kuma jami'an gwamnatin ta Musulunci, suna da alhakin kare manufofin al'umma da jin dadinsu, a takaice dai za su kasance abin tambaya a gaba ga Allah da kuma al'umma, don da man a zabe su ne a matsayin masu hidima wa al'umma, ba masu zalunta da kuma wulakanta su ba. Babu shakka, idan muka yi dubi da kyau cikin maganganu, wasiku da kuma tattaunawan da Imam Husaini (a.s) ya yi, bugu da kari kan irin yanayi na siyasa, tattalin arziki da zamantakewa da ake ciki a wancan lokacin, to lalle za mu iya fahimtar wasu al'amurra kamar haka: (1). Hukumar zaluncin Umayyawa ta wancan lokacin tana zaluntar al'umma da kuma amfani da iko da karfin mulki ta hanyar da ba ta dace ba. Wasu 'yan tsirarru ne kawai suke amfanuwa da dukiyar al'umma. Wata jam'iyya ta kabila guda ce kawai take wasa da mulki, wannan jam'iyya kuwa ita ce jam'iyyar Umayyawa. Ta kasance tana wasa da mulki da dukiyar al'umma, alhali kuwa mafi yawan al'umma an haramta musu jin dadin rayuwarsu, kai a takaice dai gwamnati da kuma dukiayr al'umma sun zamanto kaya ne kawai na Umayyawa da masu goya musu baya. (2). Kisan gilla, zalunci da ta'addanci sun zama ruwan dare game duniya. (3). Ana wasa da dukiyar al'umma, kuma da dama daga cikin jami'an gwamnatin wancan lokacin ba su cancanci su zamanto masu kula da harkokin al'umma ba, saboda rashin cancanta. (4). Lalacewar dabi'a ta zamanto wani lamari da babu mai inkarinsa, rashawa da cin hanci sun game ko ina, musamman ma a bangaren jami'an gwamnati. (5). Ba a girmama duk wata doka, ta Ubangiji ce ko kuma ma ta 'yan'Adamtaka. Son rai da bukatun masu mulki shi ne ke kan gaba da shari'a da dokokin Ubangiji. (6). Gwamnati ta samar da kuma daukan nauyin wasu mutane marasa tsoron Allah don lalata hadisan Ma'aiki (s) da kuma kirkiro wasu darikoki irin su al-Mujabbira (masu akidar cewa dukkan ayyukan 'yan'Adam Allah ne ya ke tilasta musu yin su) da dai sauransu don biyan bukatun Umayyawa masu mulki da kuma kare irin ayyukan da suke yi. (7). Da dai abubuwa makamantan hakan, wadanda lokaci ba zai ba mu daman kawo su ba. To amma hakika, tarihi ya bayyana mana irin lalacewar da al'umma suka yi da kuma rashin kula da dokokin Allah musammam ma daga wajen masu mulki. A saboda, muna iya ganin wajibcin da ya hau kan Imam Husaini (a.s) na ya mike tsaye wajen kawo gyara da kuma kawar da irin wannan karen tsaye da ake wa dokokin Allah da kuma na zamantakewa. A hakikanin gaskiya a irin wannan yanayi babu wani abin da ya hau kan Imam Husaini (a.s) da kuma dukkan bayin Allah face su mike tsaye don kawar da wannan mummunan yanayi. A matsayin misali, mu dauki yanayin tsaro na al'umma kawai, wanda Alkur'ani mai girma ya ba shi muhimmanci cikin fadin Madaukakin Sarki cewa: ( فَلْيَعْبُدُ رَبَّ هَذا الْبَيْتِ الذي أطْعَمَهُمْ مِنْ جُوعٍ وَ امَنَهُمْ مِنْ خوْفٍ ) (...lalle ne wanda ya kashe rai ba da wani rai ba, ko barna a cikin kasa, to kamar ya kashe mutane duka ne, kuma wanda ya raya rai, to, kamar ya rayar da mutane ne gaba daya. Kuma lalle ne, hakika, ManzanninMu, sun je musu da hujjoji bayyanannu, sa'an nan kuma lalle ne, masu yawa daga gare su, a bayan wannan, hakika masu barna ne a cikin kasa). (Suratu Kuraish: 106: 3-4) مَنْ قَتَلَ نَفْسًا بِغَيْرِ نَفْسٍ أَوْ فَسَادٍ فِي الأرْضِ فَكَأَنَّمَا قَتَلَ النَّاسَ جَميعًا ومَنْ أَحْياها فَكأَنَّمَا أحْيَا النَّاسَ جَميعًا ولَقَدْ جاءتْهُمْ رُسُلُنا بالبَيِّناتِ ثُمَّ إنَّ كَثيراً مِنْهُمْ بَعْدَ ذالكَ في الأرْضِ لَمُسْرِفُونَ "....Lalle ne wanda ya kashe rai ba da wani rai ba, ko barna a cikin kasa, to kamar ya kashe mutane duka ne, kuma wanda ya raya rai, to, kamar ya rayar da mutane ne gaba daya. Kuma lalle ne, hakika, ManzanninMu sun je musu da hujjoji bayyanannu, sa'an nan kuma lalle ne, masu yawa daga gare su, a bayan wannan, hakika, masu barna ne a cikin kasa". (Suratul Ma'ida: 5: 32) Sananne abu ne cewa masu mulkin wancan lokacin sun zare takubbansu da kuma bulalinsu don zaluntar al'umma, haka nan kuma sun bude gidajen kurkukunsu don sanya da kuma azabtar da duk wani wanda ya ki yarda ya mika musu kai. Haka nan kuma sun kasance masu tsananin kaushin hali ga masu adawa da mulkinsu na danniya, musamman ma ga mabiya Ahlulbaiti da jagororin adawa daga cikin mataimaka Hasan da Husaini (a.s). Daya daga cikin masu adawa da wannan gwamnati ya bayyana yadda yanayi ya kasance a wancan lokacin, yana mai magana da sahabbansa cewa: "Za a kashe ku, kana a sare hannuwa da kafafunku, haka nan kuma a cire muku idanuwa da karfe mai tsananin zafi. Kuma a giciye ku a jikin icen dabino, ba don komai ba sai don kauna mutanen gidan Annabinku...(5)". Misali, Mu'awiyya dan Abu Sufyan, ya kuduri aniyar ganin bayan shuwagabannin 'yan adawa da hukumarsa daga cikin mabiya Ahlulbaiti (a.s), don haka ya kashe wani adadi daga cikinsu da har ya zuwa yanzu tarihi bai tantance yawansu ba. Daga cikin su kuwa har da akwai: Daga cikin irin wadannan mutane da ya kashe akwai Hijr bn Adi, daya daga cikin fitattun sahabban Manzon Allah (s)(6). Irin kisan gilla da Mu'awiyan ya yi wa wannan bawan Allah ya sa har Imam Husaini (a.s) ya rubuta wa Mu'awiyya wasika yana bayyana matsayin wannan bawan Allah, kamar haka: Ashe ba kai ne ka kashe Hijr dan kabilar Kinda tare da sahabbansa, wadanda suke yin Allah wadai da zalunci, mutanen da suke ganin abin da ake aikatawa a halin yanzu a matsayin kafirce wa imani, sannan kuma ba sa jin tsoron zargin mai zargi ba? Ka kashe su cikin mummunan yanayi, bayan ka yi alkawarin ba su aminci da tsaro (yana mai nuni da sashi na biyar na yarjejeniyar sulhun da aka cimma tsakanin Imam Hasan da Mu'awiyya), kan cewa ba za ka kama su da laifi kan abin da ya gudana tsakaninka da su, ko kuma kan wata gaba da kake yi da su ba.....(7)". Mu'awiyya dai ya kashe Hijr bn Adi ne tare da wasu sahabbansa, saboda nuna adawa da rashin amincewa da suka yi ga hukumarsa da kuma yarda da jagorancin Imam Ali da 'ya'yansa (a.s) da suka yi. Sahabban Hijr din su ne: 1- Sharik bn Shaddad al-Hadhrami. 2- Sayfi bn Shaddad al-Shaibani. 3- Abdurrahman bn Hassan al-Inzi. 4- Kabisah bn Rabi'ah al-Ibsi. 5- Kidam bn Hayyan al-Inzi 6- Mihriz bn Shihab bn Bujayr bn Sufyan bn Khalid bn Munkir al-Tamimi. Baya ga wadannan kuma, Mu'awiyya ya kashe wasu daga cikin manyan mutane masu fadi a ji wadanda suka mika kansu ga Imam Ali da kuma 'ya'yansa (a.s), daga cikinsu kuwa akwai: 1- Amru bn al-Humk al-Khuza'iy: Shi sahabi ne, muhajiri, wanda yake da matsayi mai girma a wajen Manzon Allah (s.a.w.a), an kashe shi ne a garin Musil, aka gutsure kansa da wucewa da shi zuwa birnin Damaskus, fadar Mu'awiyya. Kansa dai shi ne kai na farko a tarihin Musulunci da aka dauka daga wani gari zuwa wani gari. Daga baya kuma sai fadawan Mu'awiyya suka kai kan ga matarsa wacce ita ma take daure a kurkuku da nufin kara cutar da ita, to amma koda suka wurga kan a kan cinyanta sai ta rungume shi tana sumbantar bakinsa, tana mai cewa: "Kun boye min shi na tsawon lokaci, kafin kuka miko min shi matacce a matsayin kyauta, to maraba da wannan kyauta da ba za a taba wulakanta ta ko kuma kinta ba(8)". 2- Abullah bn Yahya al-Hadhrami da sahabbansa. 3- Rashid al-Hujari, wanda aka gutsure hannuwa da kafafunsa alhali yana raye. 4- Juwairiyya bn Musahhir al-Abdi. 5- Awfar bn Hussain, shi ne mutum na farko da Ziyad ya kashe saboda muhawarar da ta shiga tsakaninsu, da farko dai Ziyad ya tambaye shi kan Usman da Mu'awiyya sai ya ba shi amsar da ba ta yi wa Ziyad din dadi ba, daga nan kuma ya tambaye shi me zai ce dangane da shi kansa (Ziyad), sai ya ce: "Na ji an ce ka fadi a garin Basra cewa wallahi za ka azabtar da maras laifi maimakon mai laifi, haka nan mai zuwa maimakon mai tafiya". Sai ya ce lalle na fadi haka. Sai Awfar ya ce masa: To kuwa lalle ka cakuda lamurra. Sai Ziyad ya cea: To ai wannan mai girman kan ba shi ne mafi munin kungiyar ba, daga nan sai ya kashe shi(9). Ibn Athir ya nakalto mana mummunan yanayi da zaluncin da ya gudana a garin Basra bayan sulhun da aka yi tsakanin Imam Hasan (a.s) da Mu'awiyya, kamar haka: "Bayan nada Sumrah gwamnan Basra da Ziyad ya yi na dan wani lokaci, sabon gwamnan ya kashe mutane da daman gaske. Ibn Sirrin ya ce: Sumrah ya kashe kimanin mutane dubu takwas a dan wannan lokaci na rikon kwarya. Lokacin da Ziyad ya tambaye shi ko ba ya jin tsoron cewa ya kashe mutumin da ba shi da laifi a yayin hakan, sai ya ce: 'Hakika ko da ninkin hakan na kashe ba zan ji tsoro ba'. Abu Sawari al-Adawi ya ce: 'Cikin kwana guda kawai, Sumrah ya kashe mutane arba'in da bakwai daga cikin sahabbai wadanda dukkansu mahaddata Alkur'ani mai girma ne(10)". To wannan dai shi ne yanayin da al'umma suke ciki a wancan lokaci, wanda ke nuni da irin da dabi'a da kuma tafarkin da mahukunta suke tafiyar da al'umma da shi, da kuma yadda suke yi da duk masu adawa da su daga cikin mabiya Ahlulbaiti (a.s) ko kuma sauran kungiyoyin 'yan adawa masu zaman kansu wadanda suke son ganin bayan wannan hukuma ta zalunci. Malaman tarihi sun nakalto mana irin kakkausar mayar da martani da yakin da Umayyawan suka kaddamar a kan kungiyar adawar da Imam Hasan da Husaini (a.s), jikokin Manzon Allah (s.a.w.a), suke jagoranta, da kuma kokarin wulakanta Amirul Muminin Aliyu bn Talib (a.s) da kuma da la'antarsa da masu mulkin suka sa a yi a kan mimbarori, don mutane su kyamace shi tare da 'ya'yansa da kuma mabiyansu. Al-Mas'udi ya nakalto wata muhawara da ta gudana tsakanin Mu'awiyya da Sa'ad bn Abi Wakkas, wacce take nuni da hannun Mu'awiyya cikin wannan farfaganda na kokarin zubar da mutumcin mafi daukakan sahabbai (Imam Ali), Mas'udi na cewa: "Abu Ja'afar Muhammad bn Jarir al-Tabari ya nakalto daga Muhammad bn Hamid al-Razi, daga Abi Mujahid daga Muhammad bn Ishak, daga Ibn Abi Najih yana cewa: 'Lokacin da Mu'awiyya ya tafi hajji, yayi dawafi tare da Sa'ad, bayan gama dawafin sai ya tafi inda zai karbi mutane (Dar al-Nadwa), sai ya zauna tare da Sa'ad. Zamansa ke da wuya sai ya fara zagin Ali (a.s), nan take sai Sa'ad ya matsa yana cewa: 'Ka zaunar da ni a kan shimfidarka, kana ka fara zagin Ali, wallahi, in mallaki sashi guda na falalar Ali, shi ya fi soyuwa a gare ni a kan abin da rana ta fito a kansa (dukkan duniya), wallahi in zamanto sirikin Manzon Allah (s.a.w.a) da kuma samun da irin wanda Ali ya samu, shi ya fi soyuwa a gare ni a kan in mallaki dukkan abin da rana ta fito a kansa. Wallahi, da Manzon Allah (s.a.w.a) ya fada a kaina abin da ya fadi wa Ali ranar Khaibar ("Gobe zan ba da tuta ga wani mutum da Allah da ManzonSa suke sonsa, shi ma kuma yake son Allah da ManzonSa, tabbatacce ba mai gudu ba, Allah Zai ba da nasara a hannunsa"), shi ya fi soyuwa a gare ni kan in mallaki abin da rana ta fito a kansa. Wallahi, da Manzon Allah (s.a.w.a) ya fadi a kaina abin da ya fadi a kan Ali ranar Tabuka, ("Ashe ba ka yarda ka kasance a gare ni kamar yadda Haruna ya kasance ga Musa ba, sai dai kawai babu Annabi a bayana"), shi ya fi soyuwa a gare ni sama da in mallaki abin da rana ta fito a kansa, lalle ba zan sake shiga gidanka matukar ina raye ba, sai yayi tafiyarsa(11). Ibn Athir ma ya ce: "Wata rana Bisr bn Arta'ah ya kasance a gidan Mu'awiyya sai ya fadi mummunar kalma a kan Imam Ali (a.s), nan take sai Zayd bn Umar bn al-Khattab da mahaifiyarsa Ummu Khultoom bint Ali suka buge shi da sanda har suka raunana shi(12)". Haka nan kuma ya nakalto cewa: "Lokacin da aka nada Mughira gwamnan Kufa, ya aike da Shihab zuwa garin Rayyu a matsayin mai kula da garin, alhali kuwa ya kasance mai yawaita zagin Ali a kan mimbari, kuma haka ya ci gaba da yi har lokacin da Ziyad ya karbi jagorancin garin Kufa(13)". "Wata rana Ziyad ya tara mutanen Kufa a fadarsa inda ya tilasta musu la'antar Ali, wanda kuwa ya kiya, sai ya kashe shi". Wannan yanayi na zagin Aliyu bn Abi Talib (a.s) dai ya ci gaba har lokacin da Umar bn Abdul'Aziz ya dare karagar mulki, inda ya hana hakan da kuma yin kwaskwa-rima ga jami'an gwamnati. Al-Mas'udi ya ci gaba da cewa: "Umar dai ya kasance mutum mai tsantsaini da kaskantar da kai. Ya sallami jami'an gwamnatin Umayyawa wacce ta wuce da kuma sanya wasu wadanda suke na kirki, wadanda suke bin tafarkinsa na gudanar da al'amurra. Shi ne wanda ya kawo karshen la'antar Ali (a.s) da ake yi akan mimbarori, da maye gurbin hakan da wannan aya ta Alkur'ani mai girma: ( ربَّنا أغفرلنا ولإخواننا الذين سبقونا بالإيمان ولا تجعل في قلوبنا غلاًّ للذين أمنوا' ربّنا إنَّك غفور رحيم ) "Ya Ubangijinmu! Ka yi mana gafara da kuma 'yan'uwanmu, wadanda suka riga mu yin imani, kada Ka sanya wani kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jin kai".(Suratul Hashr: 59:10). Wasu kuma suka ce wannan ayar ce ya sanya maimakon la'antar da ake wa Ali (a.s): ( إنّ الله يأْمر بالعدل والإحسان وايتاء ذي القربى وينهى عن الفحشاء والمنكر والبغي ) "Lalle Allah na yin umurni da adalci da kyautatawa, da bai wa ma'abucin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka ki da rarrabe jama'a...". (Suratun Nahl: 16:90). Wasu kuma suka ce dukkan biyun ne ya sanya, kuma al'umma suka ci gaba da amfani da su a hudubobi har zuwa yau(14)". Idan muka bar dalilan da suka rurata wutan wannan yunkuri da kuma karfin 'yan adawa, da suke kira ga gudanar da hukumce-hukumcen adalci da daidaitawa tsakanin al'umma da Musulunci ya ke kira zuwa gare shi, da girmama nufin al'umma da kuma riko da koyarwa da kuma akidun Musulunci wajen mu'amala ta siyasa da sauran al'umma. Haka nan kuma idan muka rufe ido kan hakan, muka kuma yi darasin yanayin tattalin arziki na wancan lokacin da kuma yadda mahukuntan suka yi karen tsaye wa tsarin rabon tattalin arziki na Musulunci wanda yake kira zuwa ga daidaituwa wajen rarraba dukiya, haramcin boye kayayyaki, wajibcin daukan nauyi da biyan bukatun marasa galihu, bugu da kari kan matsaloli na tsaro, to za mu ga cewa duk wadannan abubuwa sun kasance dalilai masu karfi na motsa zukatan al'umma da kuma matsowa kusa ga Imam Husaini (a.s) don jagorantarsu wajen kawar da irin wannan tsari. Hakika marasa galihu daga cikin al'umma sun fara kosawa da yadda ake take hakkokinsu da kuma irin tsananin talauci da suke fama da shi, a gefe guda kuma wasu 'yan tsiraru suna wasa da dukiyoyinsu, duk kuwa da cewa Allah Madaukakin Sarki Ya yi tsokaci kan hakan: ( والَّذِينَ يَكْنزون الذَّهَبَ والفِضةَ ولا يُنْفِقُونها في سبيلِ اللهِ فَبَشِّرهُمْ بِعَذابٍ أليمٍ ) "Kuma wadanda suke taskacewar zinariya da azurfa, kuma ba su ciyar da ita a cikin hanyar Allah, to, ka yi musu bushara da azaba mai radadi". (Suratul Tauba: 9:34). ما أفاءَ اللهُ على رسولِهِ من أهْلِ القرى فلِلَّهِ وللرَّسُولِ ولِذي القُربى واليَتامى والمَسَاكِين وابنِ السَّبيلِ كَي لايكونَ دولةً بينَ الأغْنياءِ منْكمْ وما اتَاكُم الرَّسولَُ فخُذوهُ وما نهاكمْ غنهُ فانتَهوا واتَّقُوا اللهَ إنَّ اللهَ شَديدُ الْعِقَابِ "Abin da Allah Ya sanya shi ganima ga ManzonSa daga mutanen kauyukan nan, to, na, Allah ne, kuma na ManzonSa ne, kuma na masu dangantaka da maraya da miskinai da dan hanya (matafiyi) ne, domin kada ya kasance abin shawagi a tsakanin mawadata daga cikinku, kuma abin da Manzo ya ba ku, to, ku kama shi, kuma abin da ya hane ku, to, ku bar shi. Kuma ku bi Allah da takawa. Lalle Allah, Mai tsananin ukuba ne". . (Suratul Hashri: 59:7). Hakika tarihi ya siffanta mana yadda yanayin tattalin arziki da kuma raba shi tsakanin al'umma ya kasance a wancan lokacin, wasu 'yan tsiraru ne suka mallake dimbin arzikin al'umma. A matsayin misali, tarihin ya bayyana mana sunayen wasu mutane wadanda suka wawuri dukiyoyin al'umma saboda alakar da suke da ita da gidan sarautar Umayyawa tun daga lokacin 'Shiryayyun Halifofi' har zuwa lokacin mulkin Yazid. Malaman tarihin sun bayyana cewa: 'Amru bn al-Aas, gwamnan Masar a lokacin Mu'awiyya, ya mallaki kadda-rorin da suka kai kimanin dinare dubu dari uku da ashirin da biyar, dirhami dubu, kayayyakin gona da suka kai dinare dubu dari biyu a Masar da kuma sanannen makeken ginin nan da ake ce al-Waht da aka kiyasta kudinsa kimanin dirhami dubu goma'. 'Haka nan kuma Abdurrahman bn Awf ya kasa gadonsa gida goma sha shida ga matayensa, inda kowace guda ta sami dirhami dubu tamanin(15)'. "Marwan bn Hakam ya kwashi kimanin dinare dubu dari biyar na kudaden shigan da aka kawo daga Afirka(16)". "Ibn al-Aas ya karbi kyautar da ta kai kimanin dirhami dubu dari(17)". "Kamar yadda Abdullah bn Khalid bn Asid ya karbi wata kyauta da ta kai kimanin dirhami dubu dari hudu(18)". "An kiyasta dukiyar Ya'ali bn Umayyah ta kai dinare dubu dari biyar, ban da basussukan da ya ke bin mutane da kuma sauran kaddarori da suka kai dinare dubu dari uku(19)". "Sa'ad bn Abi Wakkas, a lokacin mutuwarsa, ya bar kimanin dirhami dubu dari biyu da hamsin(20)". "Sa'id bn al-Musayyab ya nakalto cewa Zaid bn Thabit ya bar zinare da arzurfan da sai da gatari ake saransu da kuma dukiya da kaddarar da ta kai kimanin dinare dubu dari lokacin a lokacin mutuwarsa(21)". Wannan kadan kenan daga cikin abin da tarihi ya nakalto mana kan abubuwan da suka faru, ko da yake lamarin ba wai kawai ya takaita ba ne ga wadannan mutane da aka ambata, face dai kawai misali ne na irin mummunan yanayi na tattalin arziki da wasa da kudaden al'umma da aka yi. Wannan yanayi da ya kasa al'ummar musulmi zuwa kashi biyu, kashin fakirai marasa galihu da kuma kashin masu abin hannu wadanda suke ci da gumin al'umma, lamarin da ya saba wa tsarin Musulunci da ya yi kira zuwa ga daidaituwa tsakanin al'umma da kuma haramta satan kudaden al'umma da mallaka su ga wadansu kashi na al'ummar. Don haka irin wannan mummunan yanayi na tattalin arziki da al'umma suka shiga na daga cikin dalilan da suka motsa wutar wannan yunkuri, ta yadda kashin marasa galihu wadanda ake zalunta da kuma masu kira zuwa ga daidaito suka koma bangaren Imam Husaini (a.s), a matsayinsa na mutum guda wanda kawai zai iya gudanar da shari'a da kuma dokokin Musulunci kamar yadda ake yi a lokacin rayuwar Ma'aikin Allah (s.a.w.a). ____________ (1)- Maktal al-Husaini na al-Khawarizmi, juzu'i na 1, shafi na 88. (2)- Maktal al-Husaini na Ibn Dawus, shafi na 11. (3)- Al-Irshad na Shaikh al-Mufid, shafi na 204. (4)- Maktal al-Husain na Abdurrazak al-Mukarram, shafi na 141 da kuma na 142. (5)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi na 320 da Tarikh al-Umam wa al-Muluk na Tabari, juzu'i na 7, shafi na 104. (6)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi na 328. (7)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi na 338, ya nakalto daga Bihar al-Anwar na Allamah Majlisi, juzu'i na 10, shafi na 149. (8)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi 328. (9)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 3, shafi na 462. (10)- Kamar na sama. (11)- Muruj al-Zahab na al-Mas'udi, juzu'i na 3, shafi na 14. (12)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 4, shafi na 12. (13)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 3, shafi na 413. (14)- Muruj al-Zahab na al-Mas'udi, juzu'i na 3, shafi na 183 da 184. (15)- Kamar na sama, shafi na 23. (16)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 3, shafi na 91. (17)- Al-Ma'arif na Ibn Kutaibah al-Dinuri, shafi na 84. (18)- Kamar na sama. (19)- Muruj al-Zahab na al-Mas'udi, juzu'i na 2, shafi na 333. (20)- Dabakat na Ibn Sa'ad, juzu' i na 3, shafi na 105. (21)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 2, shafi na 333.
from Blogger https://ift.tt/2N0ZbrK
0 notes
feelsmania2019 · 5 years
Quote
Businessman ki soch :- Iss post me aap read krenge ki ek businessman ki soch kaisi honi chahiye, how to become a successful businessman in hindi ,successful businessman in hindi . Hi friends, welcome again. Mai Rohitraj ,aaj aapko apni iss post ke through ye btaunga ki ek successful businessman banne ke liye ek businessman ki soch kaisi honi chahiye. Business chahe koi bhi ho, chhota ya bada nhi hota ,usko chhota banati hai ek businessman ki soch. Thik aise hi ek business ko bada bhi ek businessman ki soch hi banati hai. Agar behter aur acha sochte ho toh chhote se level ke business ko bhi kaafi bada banaya jaa sakta hai. Believe that .Chaliye ab baat krte hai main point ki, aur main point ye hai ki ek successful businessman banne ke liye Businessman ki soch kaisi honi chahiye.              Businessman ki soch  1.Pahli soch :: Mujhe kya kerna aata hai :- Kya krna aata hai aapko, daal cheeni bechker kiryana store chala sakte ho kya, kya garments ka business ker ke acha khasa kama sakte ho ,ya paise udhaari deker sahukaari ka kaam ker sakte ho? Ek businessman ki soch pahli yhi hoti hai ki usko aakhir aata kya hai.  2.Dusri soch :: Mai jo bhi krne ki soch raha hu, kya wo sahi hai :-Jab aap koi business krne ki sochte hai, toh aapke saamne bohot se options ,alternatives hote hai. Aisi situation me aapko kisi ek suitable option ko choose krna hota hai. Ek intelligent businessman ki soch dusri yhi hoti hai ki usne jo bhi krne ka decision liya hai, Jo bhi option ko choose kiya hai, wo suitable toh hai na uske liye.  3. Mai apne business ko kitna time aur attention de sakta hu :-Time aur attention, ye dono cheeze aisi hai, agar kisi particular thing ko thik se na di jaaye toh wo particular thing hi humse bura maan jaati hai. O Hello, dear friends, agar time aur attention biwi ko na diya jaaye toh wo bhi 10 din tak bura maan jaati hai ,,hehehe 😊..ye toh business hai mere bai,, isko time attention dena kaafi important hai properly. Toh ye bhi aapko decide krna hoga ki how much time and attention you can invest in your business. Got it 😊 4.Starting me mere business ka size kitna hona chahiye :-Kuch log aise stupid hote hai, jinke pass paisa toh kaafi hota hai, per dimag bilkul bhi nhi hota. For example, ek bande ne kiryana store ka business start kiya, waise toh 1 laakh rupees me kaafi acha kiryana store start kiya jaa sakta hai, staring me, but uss paise wale bande ne start me hi 5-6 laakh rs. laga diye, kaafi bada Kiryana store khol diya. Ab start toh ker diya, Per usne apni store me product itne expensive rakh liye jitne ki big bazaar me milte hai. Aur reasonable price per na bechker mahanga bechne lga, aaspass ki society me garib log the ya middle class wale. Ab hua ye ki 2 mahino baad shop hi off ho gyi. Toh ye cheez bhi important hai ki aapke business ka size kitna hona chhote starting me.  5. Mai suru me kamayi nhi, balki mehnat krunga :-Ek successful businessman ki soch bhi yhi hoti hai ki wo suru suru me paiso ki, kamayi ki jyada parwah nhi krta, wo dekhta hai ki wo suru me kitni mehnat ker sakta hai apne business ke liye. Kyuki khud ko success tab milti hai, jab business success ho jaata hai.       Successful businessman ki soch  6.Mere business me kya koi speciality hai, ya sab ke jaisa hi hai :-Business chahe koi bhi start ker lo, 3,4 mahino baad utna kamame logoge, jitne aapke competitors kama rahe hai. Per aap ek successful businessman tab kahlaayenge, jab aap wo ker denge, jaisa aapne business start krne se pahle socha tha. Jaldi success aur unique position banane ke liye kisi bhi field me, aapme koi speciality honi chahiye, aapke business me koi speciality honi chahiye. Kyuki speciality hi aapke business ko successful bana deti hai. 7. Mai bar bar dekhunga ki kya koi kami toh nhi mere business me :-Jis tarah aapki laakho achhayiyon ke peeche koi burai chhipi hoti hai, jiski wajah se log aapko pasand nhi krte, thik waise hi kisi business ko successful banane ke liye ye bhi dekhna hota hai bar bar ki kya koi kami toh nhi hai mere business me. Aap hazaaro positive work ker lo apne business me, per ek uss negativity ko hatana bhi important hota hai, Jo aapke business ke liye thik nhi. 8.Kya mai loyal toh hu apne business ke liye :-Business chahe chhote level ka ho, ya bade level ka, utaar chadhav toh hote hi rahte hai. Agar losses dekhker, girawat dekhker aap maidan chhor gye toh aap kabhi ek businessman nhi ban sakte. Wafa ,loyalty chahe insaano ke saath rakhni ho, ya kaam dhande ke saath, rakhni toh hoti hi hai. Ek successful businessman ki soch hoti bhi yhi hai ki wo her situation me loyal rahega. 9. Mujhe mere kaam se pyar hai :-Jis Tarah 22 saal ka koi ladka beautiful si ladki ko dekhker ye sochta hai ki mai iske liye kuch bhi ker sakta hu. Thik aise hi apne business se aapko pyar krna hoga. Kyuki pyar kroge, tabhi toh usko successful banane ke liye her hadd tak jaoge. Got it 😊 10. Mera business meri responsibility hai :-Jis tarah se aapki success, aapki responsility hoti hai, thik waise hi ek businessman ki soch bhi aisi hi hoti hai ki wo apne business ko apni responsibility samajhta hai.            Businessman ki soch  11. Mai apni industry ko impress nhi, balki apni industry me khud ko improve krta rahunga :-Mostly businessman apne business ki particular industry me ek achi position banane ke liye, apne rivals, aur apni industry ko impress krne ki sochte rahte hai. Impression banane se acha hai, khud ke business ko improve krte raho. Baaki toh sab waise hi impress Ho jaayeng 12. Mai apne liye nhi, balki apne kaam ke liye kaam krunga :-Jitne bhi toppers hote hai, chahe wo koi student ho, ya kisi bhi particular field ka koi khiladi, uski mentality yhi hoti hai, wo apne liye apna kaam nhi krta, balki apne kaam ke liye kaam kerta hai. Thik aise hi ek businessman ki soch bhi aisi hi hoti hai ki wo ye nhi dekhta ki usne kya paaya apne kaam se, balki ye dekhta hai ki usne kya diya apne kaam ko. Kyuki hum khud ko toh thode se hi happy bhi rakh sakte hai, aur satisfy bhi. Per apne kaam ko bhi toh satisfy n happy rakhna hota hai ..Uske liye acha aur behter sochker. Aur ek successful businessman ki soch honi bhi yhi chahiye . My dear loving friends, I hope ,,ye article padhker aapne bohot kuch acha sikha abhi. Aur aapne jo time diya yha per, wo sahi maayne me invest hua. Aapke Kisi relative ya friend ko bhi ye article share jarur kare. Take care ,stay blessed, stay inspired 😊👍 This article was about businessman ki soch, successful business in hindi, how to become a successful businessman in hindi              Businessman ki soch 
http://www.feelsmania.com/2019/05/businessman-ki-soch-how-to-become-a-successful-businessman-in-hindi.html
0 notes
Photo
Tumblr media
This weekend we were down in Central Hawkes Bay staying at Kairakau Beach with friends. Sunday morning saw me crawl out of bed with less than 10 minutes to sunrise and go for a swift walk down to the beach with my trusty travel camera, the @fujifilmnz X-T20. Got a couple of pics coming up, firstly here's the sunrise at 6:50am with the Hine Mahanga (The Rocks) in the distance... Pure magic! The Rocks are reputed to be 36,000,000 years old. The Northern most (far left) being the Three Bears (800 yards offshore), Punch and Judy in the centre (1000 yards offshore), and Waterfall Rock in the South (1200 yards offshore). (Ref: http://ketechb.peoplesnetworknz.info/site/documents/show/75-the-story-of-kairakau @centralhawkesbaynz #hineMahanga #Kairakau #beachlife #sunrise @lynetteblackburn (at Kairakau Beach, New Zealand)
0 notes
Text
Fort Ballance
Location description
Fort Ballance Road turns off from Shelly Bay Road near the NIWA laboratory at Mahanga Bay. Fort Ballance is located at the end of the road. Note that access to the site is strictly prohibited except by permission from the New Zealand Army
After the war the site was used for army housing. When the fort was first built, bombproof, wartime accommodation for 40 men had been provided. This proved uncomfortably damp and in 1946 three 40 man huts were rapidly constructed behind the fort. The site was used for accommodation until 1990. Its use as housing saved the fort from being destroyed in the 1960s and 1970s when many of New Zealand’s ‘unsafe and unsightly’ coastal defences were demolished. Fort Ballance is now one of the best, intact examples of that string of fortifications constructed in the 1880s to defend the country from naval attack.
http://www.heritage.org.nz/the-list/details/5074
0 notes
chelseak85 · 8 years
Text
At my place: Lighting and furniture designer David Trubridge's beach house
Renowned furniture and lighting designer David Trubridge says he can't live without peace and quiet - and that's what he's found at his self-sufficient beach house at Mahanga, Hawkes Bay.  from http://www.stuff.co.nz/life-style/home-property/88583970/At-my-place-Lighting-and-furniture-designer-David-Trubridges-beach-house from Chelsea Kingston's Blog http://chelseak85.blogspot.com/2017/01/at-my-place-lighting-and-furniture.html
0 notes
gabrielarndell · 8 years
Text
At my place: Lighting and furniture designer David Trubridge’s beach house
Renowned furniture and lighting designer David Trubridge says he can’t live without peace and quiet – and that’s what he’s found at his self-sufficient beach house at Mahanga, Hawkes Bay. 
0 notes
isiyasy · 5 years
Quote
Hakika Imam Husaini (a.s) bai boye dalilin fitarsa daga birnin Madina da kuma dalilan da suka sa ya shirya yakan Yazid ba. Ya riga da ya ba da gamsasshiyar amsa ga wadanda suke so su sani. Ya bayyana manufar wannan yunkuri nasa, da kuma tafarkin da zai bi wajen yakan wannan sabuwar gwamnati ta Umayyawa. Dukkan wadannan abubuwa dai suna cikin wasikar da ya aika wa kaninsa Muhammad bn Hanafiyyah, inda ya bayyana cewa, lalacewar yanayin siyasa, zamantakewa da akidun al'umma, bugu da kari kan nauyin da ke kansa na gyaran al'umma, su ne suka sanya shi barin Madina da kuma jagorantar wannan babban yunkuri na fada da mulkin zaluncin Umayyawa. Wannan wasika ta sa tana nan kamar haka: "Ni ban fito domin girman kai ko alfahari ba, ba kuma domin barna a bayan kasa ko zalunci ba. Abin da kawai ya fito da ni shi ne neman gyara a cikin al'ummar kakana, Manzon Allah (s.a.w.a.). Ina nufin yin umurni da kyakkyawan aiki da hana mummuna, in kuma bi irin rayuwar kakana da babana.....(1)". Daga nan kuma sai ya yi bayanin dalilin da ya sa yaki yarda ya yi mubaya'a wa Yazid, da cewa: "Yazid dai lalatacce ne, mashayin giya, mai kashe rayukan da Allah Ya haramta, baya ga haka kuma yana bayyana wadannan munanan ayyuka nasa a fili. Don haka mutum kama ta ba zai taba yin bai'a wa mutum kamar Yazid ba(2)". Hakika shari'an Musulunci ya shar'anta cewa dole duk wani shugaban da zai jagoranci al'umma ya kasance yana kula da ka'idar adalci da kuma rashin nuna bambanci. Dole ne ya ba riki shari'ar Musulunci da kuma bukatun al'umma sama da komai, ba ya halalta ya yi sako-sako da dokokin Allah. Dole ne ya nesanci zalunci da kuma yin amfani da matsayinsa wajen tara kudi, jin dadi da kuma wulakanta mutane, ko kuma fifita na kusa da shi ko kuma danginsa. Sanannen abu ga Imam Husaini (as.) da kuma sauran al'umma cewa Yazid mutum ne da bai cancanci ya shugabanci al'umma ba, don kuwa mutum wanda babban burinsa shi ne yada fasadi a bayan kasa da kuma zaluntar bayin Allah. Yazid mutum ne da ya nitse cikin sabon Allah da suka da neman mata, shan giya wasa da birrai da dai duk sauran nau'o'i na wargi da wasa. Baya ga haka kuma sanannen abu ne cewa dukkan al'umma sun yarda da cewa bai kamata a ba da shugabanci ga mutumin da ya rasa siffa wacce za ta kasance abin koyi ga al'umma ba cikin ayyuka da mu'amalolinsa, sannan kuma dole ne ya kasance mutum masanin siyasa da zamani. To idan duk mun fahimci haka, to ya ya za mu yi tsammanin mutum kamar Imam Husaini (a.s) - wanda ya kasance jika ya ke wa Manzon Allah (s) kana kuma dan Fatima da Aliyu (a.s), sannan kuma burin dukkan al'umman musulmi - zai mika kai ga wannan fajiri Yazid dan Mu'awiyyah. To saboda wadannan dalilai ne ya sa Imam Husaini (a.s) ya ki ya yi bai'a wa Yazid, kuma ma ya dau makami don yakansa, kamar yadda ya bayyana wa mabiyansa a duk inda ya yada zango don su fahimci matsayarsa ta siyasa da kuma irin halin da ake ciki. A cikin wasikarsa ga mutanen Kufa, Imam Husaini (a.s) ya bayyana musu siffofin shugaba na kwarai, don ya wayar musu da kai da kuma bayyana musu wane ne ya cancanci ya zamanto shugaba. A cikin wasikar ya bayyana musu cewa: "...Na rantse, shugaba shi ne wanda ya yi shari'a da Littafin Allah, wanda ya ke gudanar da gaskiya da kuma adalci, wanda kuma yake bayyanar da hakikanin addinin gaskiya, sannan kuma wanda ya ba da kansa don Allah(3)". Haka nan kuma ya rubuta wa manyan shuwagabanni Basrah; wato Malik bn Mas'ma' al-Bukra, Al-Ahnaf bn Kais, al-Manzar bn al-Jarud, Mas'ud bn Amru, Kais bn Haitham da Amru bn Ubaid bn Mu'ammar wasika inda ya ke cewa: "...Ina kiranku zuwa ga kiyaye Littafin Allah da Sunna ManzonSa (s) da kuma aiki da su. A halin yanzu an ajiye Sunnar Annabi (s) a gefe kana kuma an raya bidi'a. Matukar kuka riki wannan kalami nawa, to ni kuwa zan ja ku zuwa ga hanya madaidaiciya. Amincin Allah ya tabbata a gare ku(4)". Hakika Imam Husaini (a.s) yana dubin gwamnati, siyasa, al'umma da kuma shugabanci ne a bisa mahanga ta Alkur'ani mai girma. To amma shi Yazid, sabanin haka, yana dubin wadannan al'amurra ne a bisa mahangar zalunci da babakere. Shugabanci, a wajen Imam Husaini (a.s), kamar wata mota ce wacce za a sanya mutane a kan tafarki shiriya da kuma isa zuwa ga hallarar Ubangiji, tafarki ne da sanya mutane a kan dokokin sama don su gina rayuwarsu akan tafarkin gasikya da kuma kyawawan dabi'u. A fahimtarsa, gwamnatin Musulunci tana karkashin kulawa ne na Musulunci da dokokinsa, wanda ita ta hakan ne za ta tsara nata dokoki da kuma ka'idoji. Haka nan kuma jami'an gwamnatin ta Musulunci, suna da alhakin kare manufofin al'umma da jin dadinsu, a takaice dai za su kasance abin tambaya a gaba ga Allah da kuma al'umma, don da man a zabe su ne a matsayin masu hidima wa al'umma, ba masu zalunta da kuma wulakanta su ba. Babu shakka, idan muka yi dubi da kyau cikin maganganu, wasiku da kuma tattaunawan da Imam Husaini (a.s) ya yi, bugu da kari kan irin yanayi na siyasa, tattalin arziki da zamantakewa da ake ciki a wancan lokacin, to lalle za mu iya fahimtar wasu al'amurra kamar haka: (1). Hukumar zaluncin Umayyawa ta wancan lokacin tana zaluntar al'umma da kuma amfani da iko da karfin mulki ta hanyar da ba ta dace ba. Wasu 'yan tsirarru ne kawai suke amfanuwa da dukiyar al'umma. Wata jam'iyya ta kabila guda ce kawai take wasa da mulki, wannan jam'iyya kuwa ita ce jam'iyyar Umayyawa. Ta kasance tana wasa da mulki da dukiyar al'umma, alhali kuwa mafi yawan al'umma an haramta musu jin dadin rayuwarsu, kai a takaice dai gwamnati da kuma dukiayr al'umma sun zamanto kaya ne kawai na Umayyawa da masu goya musu baya. (2). Kisan gilla, zalunci da ta'addanci sun zama ruwan dare game duniya. (3). Ana wasa da dukiyar al'umma, kuma da dama daga cikin jami'an gwamnatin wancan lokacin ba su cancanci su zamanto masu kula da harkokin al'umma ba, saboda rashin cancanta. (4). Lalacewar dabi'a ta zamanto wani lamari da babu mai inkarinsa, rashawa da cin hanci sun game ko ina, musamman ma a bangaren jami'an gwamnati. (5). Ba a girmama duk wata doka, ta Ubangiji ce ko kuma ma ta 'yan'Adamtaka. Son rai da bukatun masu mulki shi ne ke kan gaba da shari'a da dokokin Ubangiji. (6). Gwamnati ta samar da kuma daukan nauyin wasu mutane marasa tsoron Allah don lalata hadisan Ma'aiki (s) da kuma kirkiro wasu darikoki irin su al-Mujabbira (masu akidar cewa dukkan ayyukan 'yan'Adam Allah ne ya ke tilasta musu yin su) da dai sauransu don biyan bukatun Umayyawa masu mulki da kuma kare irin ayyukan da suke yi. (7). Da dai abubuwa makamantan hakan, wadanda lokaci ba zai ba mu daman kawo su ba. To amma hakika, tarihi ya bayyana mana irin lalacewar da al'umma suka yi da kuma rashin kula da dokokin Allah musammam ma daga wajen masu mulki. A saboda, muna iya ganin wajibcin da ya hau kan Imam Husaini (a.s) na ya mike tsaye wajen kawo gyara da kuma kawar da irin wannan karen tsaye da ake wa dokokin Allah da kuma na zamantakewa. A hakikanin gaskiya a irin wannan yanayi babu wani abin da ya hau kan Imam Husaini (a.s) da kuma dukkan bayin Allah face su mike tsaye don kawar da wannan mummunan yanayi. A matsayin misali, mu dauki yanayin tsaro na al'umma kawai, wanda Alkur'ani mai girma ya ba shi muhimmanci cikin fadin Madaukakin Sarki cewa: ( فَلْيَعْبُدُ رَبَّ هَذا الْبَيْتِ الذي أطْعَمَهُمْ مِنْ جُوعٍ وَ امَنَهُمْ مِنْ خوْفٍ ) (...lalle ne wanda ya kashe rai ba da wani rai ba, ko barna a cikin kasa, to kamar ya kashe mutane duka ne, kuma wanda ya raya rai, to, kamar ya rayar da mutane ne gaba daya. Kuma lalle ne, hakika, ManzanninMu, sun je musu da hujjoji bayyanannu, sa'an nan kuma lalle ne, masu yawa daga gare su, a bayan wannan, hakika masu barna ne a cikin kasa). (Suratu Kuraish: 106: 3-4) مَنْ قَتَلَ نَفْسًا بِغَيْرِ نَفْسٍ أَوْ فَسَادٍ فِي الأرْضِ فَكَأَنَّمَا قَتَلَ النَّاسَ جَميعًا ومَنْ أَحْياها فَكأَنَّمَا أحْيَا النَّاسَ جَميعًا ولَقَدْ جاءتْهُمْ رُسُلُنا بالبَيِّناتِ ثُمَّ إنَّ كَثيراً مِنْهُمْ بَعْدَ ذالكَ في الأرْضِ لَمُسْرِفُونَ "....Lalle ne wanda ya kashe rai ba da wani rai ba, ko barna a cikin kasa, to kamar ya kashe mutane duka ne, kuma wanda ya raya rai, to, kamar ya rayar da mutane ne gaba daya. Kuma lalle ne, hakika, ManzanninMu sun je musu da hujjoji bayyanannu, sa'an nan kuma lalle ne, masu yawa daga gare su, a bayan wannan, hakika, masu barna ne a cikin kasa". (Suratul Ma'ida: 5: 32) Sananne abu ne cewa masu mulkin wancan lokacin sun zare takubbansu da kuma bulalinsu don zaluntar al'umma, haka nan kuma sun bude gidajen kurkukunsu don sanya da kuma azabtar da duk wani wanda ya ki yarda ya mika musu kai. Haka nan kuma sun kasance masu tsananin kaushin hali ga masu adawa da mulkinsu na danniya, musamman ma ga mabiya Ahlulbaiti da jagororin adawa daga cikin mataimaka Hasan da Husaini (a.s). Daya daga cikin masu adawa da wannan gwamnati ya bayyana yadda yanayi ya kasance a wancan lokacin, yana mai magana da sahabbansa cewa: "Za a kashe ku, kana a sare hannuwa da kafafunku, haka nan kuma a cire muku idanuwa da karfe mai tsananin zafi. Kuma a giciye ku a jikin icen dabino, ba don komai ba sai don kauna mutanen gidan Annabinku...(5)". Misali, Mu'awiyya dan Abu Sufyan, ya kuduri aniyar ganin bayan shuwagabannin 'yan adawa da hukumarsa daga cikin mabiya Ahlulbaiti (a.s), don haka ya kashe wani adadi daga cikinsu da har ya zuwa yanzu tarihi bai tantance yawansu ba. Daga cikin su kuwa har da akwai: Daga cikin irin wadannan mutane da ya kashe akwai Hijr bn Adi, daya daga cikin fitattun sahabban Manzon Allah (s)(6). Irin kisan gilla da Mu'awiyan ya yi wa wannan bawan Allah ya sa har Imam Husaini (a.s) ya rubuta wa Mu'awiyya wasika yana bayyana matsayin wannan bawan Allah, kamar haka: Ashe ba kai ne ka kashe Hijr dan kabilar Kinda tare da sahabbansa, wadanda suke yin Allah wadai da zalunci, mutanen da suke ganin abin da ake aikatawa a halin yanzu a matsayin kafirce wa imani, sannan kuma ba sa jin tsoron zargin mai zargi ba? Ka kashe su cikin mummunan yanayi, bayan ka yi alkawarin ba su aminci da tsaro (yana mai nuni da sashi na biyar na yarjejeniyar sulhun da aka cimma tsakanin Imam Hasan da Mu'awiyya), kan cewa ba za ka kama su da laifi kan abin da ya gudana tsakaninka da su, ko kuma kan wata gaba da kake yi da su ba.....(7)". Mu'awiyya dai ya kashe Hijr bn Adi ne tare da wasu sahabbansa, saboda nuna adawa da rashin amincewa da suka yi ga hukumarsa da kuma yarda da jagorancin Imam Ali da 'ya'yansa (a.s) da suka yi. Sahabban Hijr din su ne: 1- Sharik bn Shaddad al-Hadhrami. 2- Sayfi bn Shaddad al-Shaibani. 3- Abdurrahman bn Hassan al-Inzi. 4- Kabisah bn Rabi'ah al-Ibsi. 5- Kidam bn Hayyan al-Inzi 6- Mihriz bn Shihab bn Bujayr bn Sufyan bn Khalid bn Munkir al-Tamimi. Baya ga wadannan kuma, Mu'awiyya ya kashe wasu daga cikin manyan mutane masu fadi a ji wadanda suka mika kansu ga Imam Ali da kuma 'ya'yansa (a.s), daga cikinsu kuwa akwai: 1- Amru bn al-Humk al-Khuza'iy: Shi sahabi ne, muhajiri, wanda yake da matsayi mai girma a wajen Manzon Allah (s.a.w.a), an kashe shi ne a garin Musil, aka gutsure kansa da wucewa da shi zuwa birnin Damaskus, fadar Mu'awiyya. Kansa dai shi ne kai na farko a tarihin Musulunci da aka dauka daga wani gari zuwa wani gari. Daga baya kuma sai fadawan Mu'awiyya suka kai kan ga matarsa wacce ita ma take daure a kurkuku da nufin kara cutar da ita, to amma koda suka wurga kan a kan cinyanta sai ta rungume shi tana sumbantar bakinsa, tana mai cewa: "Kun boye min shi na tsawon lokaci, kafin kuka miko min shi matacce a matsayin kyauta, to maraba da wannan kyauta da ba za a taba wulakanta ta ko kuma kinta ba(8)". 2- Abullah bn Yahya al-Hadhrami da sahabbansa. 3- Rashid al-Hujari, wanda aka gutsure hannuwa da kafafunsa alhali yana raye. 4- Juwairiyya bn Musahhir al-Abdi. 5- Awfar bn Hussain, shi ne mutum na farko da Ziyad ya kashe saboda muhawarar da ta shiga tsakaninsu, da farko dai Ziyad ya tambaye shi kan Usman da Mu'awiyya sai ya ba shi amsar da ba ta yi wa Ziyad din dadi ba, daga nan kuma ya tambaye shi me zai ce dangane da shi kansa (Ziyad), sai ya ce: "Na ji an ce ka fadi a garin Basra cewa wallahi za ka azabtar da maras laifi maimakon mai laifi, haka nan mai zuwa maimakon mai tafiya". Sai ya ce lalle na fadi haka. Sai Awfar ya ce masa: To kuwa lalle ka cakuda lamurra. Sai Ziyad ya cea: To ai wannan mai girman kan ba shi ne mafi munin kungiyar ba, daga nan sai ya kashe shi(9). Ibn Athir ya nakalto mana mummunan yanayi da zaluncin da ya gudana a garin Basra bayan sulhun da aka yi tsakanin Imam Hasan (a.s) da Mu'awiyya, kamar haka: "Bayan nada Sumrah gwamnan Basra da Ziyad ya yi na dan wani lokaci, sabon gwamnan ya kashe mutane da daman gaske. Ibn Sirrin ya ce: Sumrah ya kashe kimanin mutane dubu takwas a dan wannan lokaci na rikon kwarya. Lokacin da Ziyad ya tambaye shi ko ba ya jin tsoron cewa ya kashe mutumin da ba shi da laifi a yayin hakan, sai ya ce: 'Hakika ko da ninkin hakan na kashe ba zan ji tsoro ba'. Abu Sawari al-Adawi ya ce: 'Cikin kwana guda kawai, Sumrah ya kashe mutane arba'in da bakwai daga cikin sahabbai wadanda dukkansu mahaddata Alkur'ani mai girma ne(10)". To wannan dai shi ne yanayin da al'umma suke ciki a wancan lokaci, wanda ke nuni da irin da dabi'a da kuma tafarkin da mahukunta suke tafiyar da al'umma da shi, da kuma yadda suke yi da duk masu adawa da su daga cikin mabiya Ahlulbaiti (a.s) ko kuma sauran kungiyoyin 'yan adawa masu zaman kansu wadanda suke son ganin bayan wannan hukuma ta zalunci. Malaman tarihi sun nakalto mana irin kakkausar mayar da martani da yakin da Umayyawan suka kaddamar a kan kungiyar adawar da Imam Hasan da Husaini (a.s), jikokin Manzon Allah (s.a.w.a), suke jagoranta, da kuma kokarin wulakanta Amirul Muminin Aliyu bn Talib (a.s) da kuma da la'antarsa da masu mulkin suka sa a yi a kan mimbarori, don mutane su kyamace shi tare da 'ya'yansa da kuma mabiyansu. Al-Mas'udi ya nakalto wata muhawara da ta gudana tsakanin Mu'awiyya da Sa'ad bn Abi Wakkas, wacce take nuni da hannun Mu'awiyya cikin wannan farfaganda na kokarin zubar da mutumcin mafi daukakan sahabbai (Imam Ali), Mas'udi na cewa: "Abu Ja'afar Muhammad bn Jarir al-Tabari ya nakalto daga Muhammad bn Hamid al-Razi, daga Abi Mujahid daga Muhammad bn Ishak, daga Ibn Abi Najih yana cewa: 'Lokacin da Mu'awiyya ya tafi hajji, yayi dawafi tare da Sa'ad, bayan gama dawafin sai ya tafi inda zai karbi mutane (Dar al-Nadwa), sai ya zauna tare da Sa'ad. Zamansa ke da wuya sai ya fara zagin Ali (a.s), nan take sai Sa'ad ya matsa yana cewa: 'Ka zaunar da ni a kan shimfidarka, kana ka fara zagin Ali, wallahi, in mallaki sashi guda na falalar Ali, shi ya fi soyuwa a gare ni a kan abin da rana ta fito a kansa (dukkan duniya), wallahi in zamanto sirikin Manzon Allah (s.a.w.a) da kuma samun da irin wanda Ali ya samu, shi ya fi soyuwa a gare ni a kan in mallaki dukkan abin da rana ta fito a kansa. Wallahi, da Manzon Allah (s.a.w.a) ya fada a kaina abin da ya fadi wa Ali ranar Khaibar ("Gobe zan ba da tuta ga wani mutum da Allah da ManzonSa suke sonsa, shi ma kuma yake son Allah da ManzonSa, tabbatacce ba mai gudu ba, Allah Zai ba da nasara a hannunsa"), shi ya fi soyuwa a gare ni kan in mallaki abin da rana ta fito a kansa. Wallahi, da Manzon Allah (s.a.w.a) ya fadi a kaina abin da ya fadi a kan Ali ranar Tabuka, ("Ashe ba ka yarda ka kasance a gare ni kamar yadda Haruna ya kasance ga Musa ba, sai dai kawai babu Annabi a bayana"), shi ya fi soyuwa a gare ni sama da in mallaki abin da rana ta fito a kansa, lalle ba zan sake shiga gidanka matukar ina raye ba, sai yayi tafiyarsa(11). Ibn Athir ma ya ce: "Wata rana Bisr bn Arta'ah ya kasance a gidan Mu'awiyya sai ya fadi mummunar kalma a kan Imam Ali (a.s), nan take sai Zayd bn Umar bn al-Khattab da mahaifiyarsa Ummu Khultoom bint Ali suka buge shi da sanda har suka raunana shi(12)". Haka nan kuma ya nakalto cewa: "Lokacin da aka nada Mughira gwamnan Kufa, ya aike da Shihab zuwa garin Rayyu a matsayin mai kula da garin, alhali kuwa ya kasance mai yawaita zagin Ali a kan mimbari, kuma haka ya ci gaba da yi har lokacin da Ziyad ya karbi jagorancin garin Kufa(13)". "Wata rana Ziyad ya tara mutanen Kufa a fadarsa inda ya tilasta musu la'antar Ali, wanda kuwa ya kiya, sai ya kashe shi". Wannan yanayi na zagin Aliyu bn Abi Talib (a.s) dai ya ci gaba har lokacin da Umar bn Abdul'Aziz ya dare karagar mulki, inda ya hana hakan da kuma yin kwaskwa-rima ga jami'an gwamnati. Al-Mas'udi ya ci gaba da cewa: "Umar dai ya kasance mutum mai tsantsaini da kaskantar da kai. Ya sallami jami'an gwamnatin Umayyawa wacce ta wuce da kuma sanya wasu wadanda suke na kirki, wadanda suke bin tafarkinsa na gudanar da al'amurra. Shi ne wanda ya kawo karshen la'antar Ali (a.s) da ake yi akan mimbarori, da maye gurbin hakan da wannan aya ta Alkur'ani mai girma: ( ربَّنا أغفرلنا ولإخواننا الذين سبقونا بالإيمان ولا تجعل في قلوبنا غلاًّ للذين أمنوا' ربّنا إنَّك غفور رحيم ) "Ya Ubangijinmu! Ka yi mana gafara da kuma 'yan'uwanmu, wadanda suka riga mu yin imani, kada Ka sanya wani kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jin kai".(Suratul Hashr: 59:10). Wasu kuma suka ce wannan ayar ce ya sanya maimakon la'antar da ake wa Ali (a.s): ( إنّ الله يأْمر بالعدل والإحسان وايتاء ذي القربى وينهى عن الفحشاء والمنكر والبغي ) "Lalle Allah na yin umurni da adalci da kyautatawa, da bai wa ma'abucin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka ki da rarrabe jama'a...". (Suratun Nahl: 16:90). Wasu kuma suka ce dukkan biyun ne ya sanya, kuma al'umma suka ci gaba da amfani da su a hudubobi har zuwa yau(14)". Idan muka bar dalilan da suka rurata wutan wannan yunkuri da kuma karfin 'yan adawa, da suke kira ga gudanar da hukumce-hukumcen adalci da daidaitawa tsakanin al'umma da Musulunci ya ke kira zuwa gare shi, da girmama nufin al'umma da kuma riko da koyarwa da kuma akidun Musulunci wajen mu'amala ta siyasa da sauran al'umma. Haka nan kuma idan muka rufe ido kan hakan, muka kuma yi darasin yanayin tattalin arziki na wancan lokacin da kuma yadda mahukuntan suka yi karen tsaye wa tsarin rabon tattalin arziki na Musulunci wanda yake kira zuwa ga daidaituwa wajen rarraba dukiya, haramcin boye kayayyaki, wajibcin daukan nauyi da biyan bukatun marasa galihu, bugu da kari kan matsaloli na tsaro, to za mu ga cewa duk wadannan abubuwa sun kasance dalilai masu karfi na motsa zukatan al'umma da kuma matsowa kusa ga Imam Husaini (a.s) don jagorantarsu wajen kawar da irin wannan tsari. Hakika marasa galihu daga cikin al'umma sun fara kosawa da yadda ake take hakkokinsu da kuma irin tsananin talauci da suke fama da shi, a gefe guda kuma wasu 'yan tsiraru suna wasa da dukiyoyinsu, duk kuwa da cewa Allah Madaukakin Sarki Ya yi tsokaci kan hakan: ( والَّذِينَ يَكْنزون الذَّهَبَ والفِضةَ ولا يُنْفِقُونها في سبيلِ اللهِ فَبَشِّرهُمْ بِعَذابٍ أليمٍ ) "Kuma wadanda suke taskacewar zinariya da azurfa, kuma ba su ciyar da ita a cikin hanyar Allah, to, ka yi musu bushara da azaba mai radadi". (Suratul Tauba: 9:34). ما أفاءَ اللهُ على رسولِهِ من أهْلِ القرى فلِلَّهِ وللرَّسُولِ ولِذي القُربى واليَتامى والمَسَاكِين وابنِ السَّبيلِ كَي لايكونَ دولةً بينَ الأغْنياءِ منْكمْ وما اتَاكُم الرَّسولَُ فخُذوهُ وما نهاكمْ غنهُ فانتَهوا واتَّقُوا اللهَ إنَّ اللهَ شَديدُ الْعِقَابِ "Abin da Allah Ya sanya shi ganima ga ManzonSa daga mutanen kauyukan nan, to, na, Allah ne, kuma na ManzonSa ne, kuma na masu dangantaka da maraya da miskinai da dan hanya (matafiyi) ne, domin kada ya kasance abin shawagi a tsakanin mawadata daga cikinku, kuma abin da Manzo ya ba ku, to, ku kama shi, kuma abin da ya hane ku, to, ku bar shi. Kuma ku bi Allah da takawa. Lalle Allah, Mai tsananin ukuba ne". . (Suratul Hashri: 59:7). Hakika tarihi ya siffanta mana yadda yanayin tattalin arziki da kuma raba shi tsakanin al'umma ya kasance a wancan lokacin, wasu 'yan tsiraru ne suka mallake dimbin arzikin al'umma. A matsayin misali, tarihin ya bayyana mana sunayen wasu mutane wadanda suka wawuri dukiyoyin al'umma saboda alakar da suke da ita da gidan sarautar Umayyawa tun daga lokacin 'Shiryayyun Halifofi' har zuwa lokacin mulkin Yazid. Malaman tarihin sun bayyana cewa: 'Amru bn al-Aas, gwamnan Masar a lokacin Mu'awiyya, ya mallaki kadda-rorin da suka kai kimanin dinare dubu dari uku da ashirin da biyar, dirhami dubu, kayayyakin gona da suka kai dinare dubu dari biyu a Masar da kuma sanannen makeken ginin nan da ake ce al-Waht da aka kiyasta kudinsa kimanin dirhami dubu goma'. 'Haka nan kuma Abdurrahman bn Awf ya kasa gadonsa gida goma sha shida ga matayensa, inda kowace guda ta sami dirhami dubu tamanin(15)'. "Marwan bn Hakam ya kwashi kimanin dinare dubu dari biyar na kudaden shigan da aka kawo daga Afirka(16)". "Ibn al-Aas ya karbi kyautar da ta kai kimanin dirhami dubu dari(17)". "Kamar yadda Abdullah bn Khalid bn Asid ya karbi wata kyauta da ta kai kimanin dirhami dubu dari hudu(18)". "An kiyasta dukiyar Ya'ali bn Umayyah ta kai dinare dubu dari biyar, ban da basussukan da ya ke bin mutane da kuma sauran kaddarori da suka kai dinare dubu dari uku(19)". "Sa'ad bn Abi Wakkas, a lokacin mutuwarsa, ya bar kimanin dirhami dubu dari biyu da hamsin(20)". "Sa'id bn al-Musayyab ya nakalto cewa Zaid bn Thabit ya bar zinare da arzurfan da sai da gatari ake saransu da kuma dukiya da kaddarar da ta kai kimanin dinare dubu dari lokacin a lokacin mutuwarsa(21)". Wannan kadan kenan daga cikin abin da tarihi ya nakalto mana kan abubuwan da suka faru, ko da yake lamarin ba wai kawai ya takaita ba ne ga wadannan mutane da aka ambata, face dai kawai misali ne na irin mummunan yanayi na tattalin arziki da wasa da kudaden al'umma da aka yi. Wannan yanayi da ya kasa al'ummar musulmi zuwa kashi biyu, kashin fakirai marasa galihu da kuma kashin masu abin hannu wadanda suke ci da gumin al'umma, lamarin da ya saba wa tsarin Musulunci da ya yi kira zuwa ga daidaituwa tsakanin al'umma da kuma haramta satan kudaden al'umma da mallaka su ga wadansu kashi na al'ummar. Don haka irin wannan mummunan yanayi na tattalin arziki da al'umma suka shiga na daga cikin dalilan da suka motsa wutar wannan yunkuri, ta yadda kashin marasa galihu wadanda ake zalunta da kuma masu kira zuwa ga daidaito suka koma bangaren Imam Husaini (a.s), a matsayinsa na mutum guda wanda kawai zai iya gudanar da shari'a da kuma dokokin Musulunci kamar yadda ake yi a lokacin rayuwar Ma'aikin Allah (s.a.w.a). ____________ (1)- Maktal al-Husaini na al-Khawarizmi, juzu'i na 1, shafi na 88. (2)- Maktal al-Husaini na Ibn Dawus, shafi na 11. (3)- Al-Irshad na Shaikh al-Mufid, shafi na 204. (4)- Maktal al-Husain na Abdurrazak al-Mukarram, shafi na 141 da kuma na 142. (5)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi na 320 da Tarikh al-Umam wa al-Muluk na Tabari, juzu'i na 7, shafi na 104. (6)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi na 328. (7)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi na 338, ya nakalto daga Bihar al-Anwar na Allamah Majlisi, juzu'i na 10, shafi na 149. (8)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi 328. (9)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 3, shafi na 462. (10)- Kamar na sama. (11)- Muruj al-Zahab na al-Mas'udi, juzu'i na 3, shafi na 14. (12)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 4, shafi na 12. (13)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 3, shafi na 413. (14)- Muruj al-Zahab na al-Mas'udi, juzu'i na 3, shafi na 183 da 184. (15)- Kamar na sama, shafi na 23. (16)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 3, shafi na 91. (17)- Al-Ma'arif na Ibn Kutaibah al-Dinuri, shafi na 84. (18)- Kamar na sama. (19)- Muruj al-Zahab na al-Mas'udi, juzu'i na 2, shafi na 333. (20)- Dabakat na Ibn Sa'ad, juzu' i na 3, shafi na 105. (21)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 2, shafi na 333.
http://www.5five-stars.com.ng/2019/09/dalilan-yunkurin-imam-husaini-as.html
0 notes
isiyasy · 5 years
Quote
Hakika Imam Husaini (a.s) bai boye dalilin fitarsa daga birnin Madina da kuma dalilan da suka sa ya shirya yakan Yazid ba. Ya riga da ya ba da gamsasshiyar amsa ga wadanda suke so su sani. Ya bayyana manufar wannan yunkuri nasa, da kuma tafarkin da zai bi wajen yakan wannan sabuwar gwamnati ta Umayyawa. Dukkan wadannan abubuwa dai suna cikin wasikar da ya aika wa kaninsa Muhammad bn Hanafiyyah, inda ya bayyana cewa, lalacewar yanayin siyasa, zamantakewa da akidun al'umma, bugu da kari kan nauyin da ke kansa na gyaran al'umma, su ne suka sanya shi barin Madina da kuma jagorantar wannan babban yunkuri na fada da mulkin zaluncin Umayyawa. Wannan wasika ta sa tana nan kamar haka: "Ni ban fito domin girman kai ko alfahari ba, ba kuma domin barna a bayan kasa ko zalunci ba. Abin da kawai ya fito da ni shi ne neman gyara a cikin al'ummar kakana, Manzon Allah (s.a.w.a.). Ina nufin yin umurni da kyakkyawan aiki da hana mummuna, in kuma bi irin rayuwar kakana da babana.....(1)". Daga nan kuma sai ya yi bayanin dalilin da ya sa yaki yarda ya yi mubaya'a wa Yazid, da cewa: "Yazid dai lalatacce ne, mashayin giya, mai kashe rayukan da Allah Ya haramta, baya ga haka kuma yana bayyana wadannan munanan ayyuka nasa a fili. Don haka mutum kama ta ba zai taba yin bai'a wa mutum kamar Yazid ba(2)". Hakika shari'an Musulunci ya shar'anta cewa dole duk wani shugaban da zai jagoranci al'umma ya kasance yana kula da ka'idar adalci da kuma rashin nuna bambanci. Dole ne ya ba riki shari'ar Musulunci da kuma bukatun al'umma sama da komai, ba ya halalta ya yi sako-sako da dokokin Allah. Dole ne ya nesanci zalunci da kuma yin amfani da matsayinsa wajen tara kudi, jin dadi da kuma wulakanta mutane, ko kuma fifita na kusa da shi ko kuma danginsa. Sanannen abu ga Imam Husaini (as.) da kuma sauran al'umma cewa Yazid mutum ne da bai cancanci ya shugabanci al'umma ba, don kuwa mutum wanda babban burinsa shi ne yada fasadi a bayan kasa da kuma zaluntar bayin Allah. Yazid mutum ne da ya nitse cikin sabon Allah da suka da neman mata, shan giya wasa da birrai da dai duk sauran nau'o'i na wargi da wasa. Baya ga haka kuma sanannen abu ne cewa dukkan al'umma sun yarda da cewa bai kamata a ba da shugabanci ga mutumin da ya rasa siffa wacce za ta kasance abin koyi ga al'umma ba cikin ayyuka da mu'amalolinsa, sannan kuma dole ne ya kasance mutum masanin siyasa da zamani. To idan duk mun fahimci haka, to ya ya za mu yi tsammanin mutum kamar Imam Husaini (a.s) - wanda ya kasance jika ya ke wa Manzon Allah (s) kana kuma dan Fatima da Aliyu (a.s), sannan kuma burin dukkan al'umman musulmi - zai mika kai ga wannan fajiri Yazid dan Mu'awiyyah. To saboda wadannan dalilai ne ya sa Imam Husaini (a.s) ya ki ya yi bai'a wa Yazid, kuma ma ya dau makami don yakansa, kamar yadda ya bayyana wa mabiyansa a duk inda ya yada zango don su fahimci matsayarsa ta siyasa da kuma irin halin da ake ciki. A cikin wasikarsa ga mutanen Kufa, Imam Husaini (a.s) ya bayyana musu siffofin shugaba na kwarai, don ya wayar musu da kai da kuma bayyana musu wane ne ya cancanci ya zamanto shugaba. A cikin wasikar ya bayyana musu cewa: "...Na rantse, shugaba shi ne wanda ya yi shari'a da Littafin Allah, wanda ya ke gudanar da gaskiya da kuma adalci, wanda kuma yake bayyanar da hakikanin addinin gaskiya, sannan kuma wanda ya ba da kansa don Allah(3)". Haka nan kuma ya rubuta wa manyan shuwagabanni Basrah; wato Malik bn Mas'ma' al-Bukra, Al-Ahnaf bn Kais, al-Manzar bn al-Jarud, Mas'ud bn Amru, Kais bn Haitham da Amru bn Ubaid bn Mu'ammar wasika inda ya ke cewa: "...Ina kiranku zuwa ga kiyaye Littafin Allah da Sunna ManzonSa (s) da kuma aiki da su. A halin yanzu an ajiye Sunnar Annabi (s) a gefe kana kuma an raya bidi'a. Matukar kuka riki wannan kalami nawa, to ni kuwa zan ja ku zuwa ga hanya madaidaiciya. Amincin Allah ya tabbata a gare ku(4)". Hakika Imam Husaini (a.s) yana dubin gwamnati, siyasa, al'umma da kuma shugabanci ne a bisa mahanga ta Alkur'ani mai girma. To amma shi Yazid, sabanin haka, yana dubin wadannan al'amurra ne a bisa mahangar zalunci da babakere. Shugabanci, a wajen Imam Husaini (a.s), kamar wata mota ce wacce za a sanya mutane a kan tafarki shiriya da kuma isa zuwa ga hallarar Ubangiji, tafarki ne da sanya mutane a kan dokokin sama don su gina rayuwarsu akan tafarkin gasikya da kuma kyawawan dabi'u. A fahimtarsa, gwamnatin Musulunci tana karkashin kulawa ne na Musulunci da dokokinsa, wanda ita ta hakan ne za ta tsara nata dokoki da kuma ka'idoji. Haka nan kuma jami'an gwamnatin ta Musulunci, suna da alhakin kare manufofin al'umma da jin dadinsu, a takaice dai za su kasance abin tambaya a gaba ga Allah da kuma al'umma, don da man a zabe su ne a matsayin masu hidima wa al'umma, ba masu zalunta da kuma wulakanta su ba. Babu shakka, idan muka yi dubi da kyau cikin maganganu, wasiku da kuma tattaunawan da Imam Husaini (a.s) ya yi, bugu da kari kan irin yanayi na siyasa, tattalin arziki da zamantakewa da ake ciki a wancan lokacin, to lalle za mu iya fahimtar wasu al'amurra kamar haka: (1). Hukumar zaluncin Umayyawa ta wancan lokacin tana zaluntar al'umma da kuma amfani da iko da karfin mulki ta hanyar da ba ta dace ba. Wasu 'yan tsirarru ne kawai suke amfanuwa da dukiyar al'umma. Wata jam'iyya ta kabila guda ce kawai take wasa da mulki, wannan jam'iyya kuwa ita ce jam'iyyar Umayyawa. Ta kasance tana wasa da mulki da dukiyar al'umma, alhali kuwa mafi yawan al'umma an haramta musu jin dadin rayuwarsu, kai a takaice dai gwamnati da kuma dukiayr al'umma sun zamanto kaya ne kawai na Umayyawa da masu goya musu baya. (2). Kisan gilla, zalunci da ta'addanci sun zama ruwan dare game duniya. (3). Ana wasa da dukiyar al'umma, kuma da dama daga cikin jami'an gwamnatin wancan lokacin ba su cancanci su zamanto masu kula da harkokin al'umma ba, saboda rashin cancanta. (4). Lalacewar dabi'a ta zamanto wani lamari da babu mai inkarinsa, rashawa da cin hanci sun game ko ina, musamman ma a bangaren jami'an gwamnati. (5). Ba a girmama duk wata doka, ta Ubangiji ce ko kuma ma ta 'yan'Adamtaka. Son rai da bukatun masu mulki shi ne ke kan gaba da shari'a da dokokin Ubangiji. (6). Gwamnati ta samar da kuma daukan nauyin wasu mutane marasa tsoron Allah don lalata hadisan Ma'aiki (s) da kuma kirkiro wasu darikoki irin su al-Mujabbira (masu akidar cewa dukkan ayyukan 'yan'Adam Allah ne ya ke tilasta musu yin su) da dai sauransu don biyan bukatun Umayyawa masu mulki da kuma kare irin ayyukan da suke yi. (7). Da dai abubuwa makamantan hakan, wadanda lokaci ba zai ba mu daman kawo su ba. To amma hakika, tarihi ya bayyana mana irin lalacewar da al'umma suka yi da kuma rashin kula da dokokin Allah musammam ma daga wajen masu mulki. A saboda, muna iya ganin wajibcin da ya hau kan Imam Husaini (a.s) na ya mike tsaye wajen kawo gyara da kuma kawar da irin wannan karen tsaye da ake wa dokokin Allah da kuma na zamantakewa. A hakikanin gaskiya a irin wannan yanayi babu wani abin da ya hau kan Imam Husaini (a.s) da kuma dukkan bayin Allah face su mike tsaye don kawar da wannan mummunan yanayi. A matsayin misali, mu dauki yanayin tsaro na al'umma kawai, wanda Alkur'ani mai girma ya ba shi muhimmanci cikin fadin Madaukakin Sarki cewa: ( فَلْيَعْبُدُ رَبَّ هَذا الْبَيْتِ الذي أطْعَمَهُمْ مِنْ جُوعٍ وَ امَنَهُمْ مِنْ خوْفٍ ) (...lalle ne wanda ya kashe rai ba da wani rai ba, ko barna a cikin kasa, to kamar ya kashe mutane duka ne, kuma wanda ya raya rai, to, kamar ya rayar da mutane ne gaba daya. Kuma lalle ne, hakika, ManzanninMu, sun je musu da hujjoji bayyanannu, sa'an nan kuma lalle ne, masu yawa daga gare su, a bayan wannan, hakika masu barna ne a cikin kasa). (Suratu Kuraish: 106: 3-4) مَنْ قَتَلَ نَفْسًا بِغَيْرِ نَفْسٍ أَوْ فَسَادٍ فِي الأرْضِ فَكَأَنَّمَا قَتَلَ النَّاسَ جَميعًا ومَنْ أَحْياها فَكأَنَّمَا أحْيَا النَّاسَ جَميعًا ولَقَدْ جاءتْهُمْ رُسُلُنا بالبَيِّناتِ ثُمَّ إنَّ كَثيراً مِنْهُمْ بَعْدَ ذالكَ في الأرْضِ لَمُسْرِفُونَ "....Lalle ne wanda ya kashe rai ba da wani rai ba, ko barna a cikin kasa, to kamar ya kashe mutane duka ne, kuma wanda ya raya rai, to, kamar ya rayar da mutane ne gaba daya. Kuma lalle ne, hakika, ManzanninMu sun je musu da hujjoji bayyanannu, sa'an nan kuma lalle ne, masu yawa daga gare su, a bayan wannan, hakika, masu barna ne a cikin kasa". (Suratul Ma'ida: 5: 32) Sananne abu ne cewa masu mulkin wancan lokacin sun zare takubbansu da kuma bulalinsu don zaluntar al'umma, haka nan kuma sun bude gidajen kurkukunsu don sanya da kuma azabtar da duk wani wanda ya ki yarda ya mika musu kai. Haka nan kuma sun kasance masu tsananin kaushin hali ga masu adawa da mulkinsu na danniya, musamman ma ga mabiya Ahlulbaiti da jagororin adawa daga cikin mataimaka Hasan da Husaini (a.s). Daya daga cikin masu adawa da wannan gwamnati ya bayyana yadda yanayi ya kasance a wancan lokacin, yana mai magana da sahabbansa cewa: "Za a kashe ku, kana a sare hannuwa da kafafunku, haka nan kuma a cire muku idanuwa da karfe mai tsananin zafi. Kuma a giciye ku a jikin icen dabino, ba don komai ba sai don kauna mutanen gidan Annabinku...(5)". Misali, Mu'awiyya dan Abu Sufyan, ya kuduri aniyar ganin bayan shuwagabannin 'yan adawa da hukumarsa daga cikin mabiya Ahlulbaiti (a.s), don haka ya kashe wani adadi daga cikinsu da har ya zuwa yanzu tarihi bai tantance yawansu ba. Daga cikin su kuwa har da akwai: Daga cikin irin wadannan mutane da ya kashe akwai Hijr bn Adi, daya daga cikin fitattun sahabban Manzon Allah (s)(6). Irin kisan gilla da Mu'awiyan ya yi wa wannan bawan Allah ya sa har Imam Husaini (a.s) ya rubuta wa Mu'awiyya wasika yana bayyana matsayin wannan bawan Allah, kamar haka: Ashe ba kai ne ka kashe Hijr dan kabilar Kinda tare da sahabbansa, wadanda suke yin Allah wadai da zalunci, mutanen da suke ganin abin da ake aikatawa a halin yanzu a matsayin kafirce wa imani, sannan kuma ba sa jin tsoron zargin mai zargi ba? Ka kashe su cikin mummunan yanayi, bayan ka yi alkawarin ba su aminci da tsaro (yana mai nuni da sashi na biyar na yarjejeniyar sulhun da aka cimma tsakanin Imam Hasan da Mu'awiyya), kan cewa ba za ka kama su da laifi kan abin da ya gudana tsakaninka da su, ko kuma kan wata gaba da kake yi da su ba.....(7)". Mu'awiyya dai ya kashe Hijr bn Adi ne tare da wasu sahabbansa, saboda nuna adawa da rashin amincewa da suka yi ga hukumarsa da kuma yarda da jagorancin Imam Ali da 'ya'yansa (a.s) da suka yi. Sahabban Hijr din su ne: 1- Sharik bn Shaddad al-Hadhrami. 2- Sayfi bn Shaddad al-Shaibani. 3- Abdurrahman bn Hassan al-Inzi. 4- Kabisah bn Rabi'ah al-Ibsi. 5- Kidam bn Hayyan al-Inzi 6- Mihriz bn Shihab bn Bujayr bn Sufyan bn Khalid bn Munkir al-Tamimi. Baya ga wadannan kuma, Mu'awiyya ya kashe wasu daga cikin manyan mutane masu fadi a ji wadanda suka mika kansu ga Imam Ali da kuma 'ya'yansa (a.s), daga cikinsu kuwa akwai: 1- Amru bn al-Humk al-Khuza'iy: Shi sahabi ne, muhajiri, wanda yake da matsayi mai girma a wajen Manzon Allah (s.a.w.a), an kashe shi ne a garin Musil, aka gutsure kansa da wucewa da shi zuwa birnin Damaskus, fadar Mu'awiyya. Kansa dai shi ne kai na farko a tarihin Musulunci da aka dauka daga wani gari zuwa wani gari. Daga baya kuma sai fadawan Mu'awiyya suka kai kan ga matarsa wacce ita ma take daure a kurkuku da nufin kara cutar da ita, to amma koda suka wurga kan a kan cinyanta sai ta rungume shi tana sumbantar bakinsa, tana mai cewa: "Kun boye min shi na tsawon lokaci, kafin kuka miko min shi matacce a matsayin kyauta, to maraba da wannan kyauta da ba za a taba wulakanta ta ko kuma kinta ba(8)". 2- Abullah bn Yahya al-Hadhrami da sahabbansa. 3- Rashid al-Hujari, wanda aka gutsure hannuwa da kafafunsa alhali yana raye. 4- Juwairiyya bn Musahhir al-Abdi. 5- Awfar bn Hussain, shi ne mutum na farko da Ziyad ya kashe saboda muhawarar da ta shiga tsakaninsu, da farko dai Ziyad ya tambaye shi kan Usman da Mu'awiyya sai ya ba shi amsar da ba ta yi wa Ziyad din dadi ba, daga nan kuma ya tambaye shi me zai ce dangane da shi kansa (Ziyad), sai ya ce: "Na ji an ce ka fadi a garin Basra cewa wallahi za ka azabtar da maras laifi maimakon mai laifi, haka nan mai zuwa maimakon mai tafiya". Sai ya ce lalle na fadi haka. Sai Awfar ya ce masa: To kuwa lalle ka cakuda lamurra. Sai Ziyad ya cea: To ai wannan mai girman kan ba shi ne mafi munin kungiyar ba, daga nan sai ya kashe shi(9). Ibn Athir ya nakalto mana mummunan yanayi da zaluncin da ya gudana a garin Basra bayan sulhun da aka yi tsakanin Imam Hasan (a.s) da Mu'awiyya, kamar haka: "Bayan nada Sumrah gwamnan Basra da Ziyad ya yi na dan wani lokaci, sabon gwamnan ya kashe mutane da daman gaske. Ibn Sirrin ya ce: Sumrah ya kashe kimanin mutane dubu takwas a dan wannan lokaci na rikon kwarya. Lokacin da Ziyad ya tambaye shi ko ba ya jin tsoron cewa ya kashe mutumin da ba shi da laifi a yayin hakan, sai ya ce: 'Hakika ko da ninkin hakan na kashe ba zan ji tsoro ba'. Abu Sawari al-Adawi ya ce: 'Cikin kwana guda kawai, Sumrah ya kashe mutane arba'in da bakwai daga cikin sahabbai wadanda dukkansu mahaddata Alkur'ani mai girma ne(10)". To wannan dai shi ne yanayin da al'umma suke ciki a wancan lokaci, wanda ke nuni da irin da dabi'a da kuma tafarkin da mahukunta suke tafiyar da al'umma da shi, da kuma yadda suke yi da duk masu adawa da su daga cikin mabiya Ahlulbaiti (a.s) ko kuma sauran kungiyoyin 'yan adawa masu zaman kansu wadanda suke son ganin bayan wannan hukuma ta zalunci. Malaman tarihi sun nakalto mana irin kakkausar mayar da martani da yakin da Umayyawan suka kaddamar a kan kungiyar adawar da Imam Hasan da Husaini (a.s), jikokin Manzon Allah (s.a.w.a), suke jagoranta, da kuma kokarin wulakanta Amirul Muminin Aliyu bn Talib (a.s) da kuma da la'antarsa da masu mulkin suka sa a yi a kan mimbarori, don mutane su kyamace shi tare da 'ya'yansa da kuma mabiyansu. Al-Mas'udi ya nakalto wata muhawara da ta gudana tsakanin Mu'awiyya da Sa'ad bn Abi Wakkas, wacce take nuni da hannun Mu'awiyya cikin wannan farfaganda na kokarin zubar da mutumcin mafi daukakan sahabbai (Imam Ali), Mas'udi na cewa: "Abu Ja'afar Muhammad bn Jarir al-Tabari ya nakalto daga Muhammad bn Hamid al-Razi, daga Abi Mujahid daga Muhammad bn Ishak, daga Ibn Abi Najih yana cewa: 'Lokacin da Mu'awiyya ya tafi hajji, yayi dawafi tare da Sa'ad, bayan gama dawafin sai ya tafi inda zai karbi mutane (Dar al-Nadwa), sai ya zauna tare da Sa'ad. Zamansa ke da wuya sai ya fara zagin Ali (a.s), nan take sai Sa'ad ya matsa yana cewa: 'Ka zaunar da ni a kan shimfidarka, kana ka fara zagin Ali, wallahi, in mallaki sashi guda na falalar Ali, shi ya fi soyuwa a gare ni a kan abin da rana ta fito a kansa (dukkan duniya), wallahi in zamanto sirikin Manzon Allah (s.a.w.a) da kuma samun da irin wanda Ali ya samu, shi ya fi soyuwa a gare ni a kan in mallaki dukkan abin da rana ta fito a kansa. Wallahi, da Manzon Allah (s.a.w.a) ya fada a kaina abin da ya fadi wa Ali ranar Khaibar ("Gobe zan ba da tuta ga wani mutum da Allah da ManzonSa suke sonsa, shi ma kuma yake son Allah da ManzonSa, tabbatacce ba mai gudu ba, Allah Zai ba da nasara a hannunsa"), shi ya fi soyuwa a gare ni kan in mallaki abin da rana ta fito a kansa. Wallahi, da Manzon Allah (s.a.w.a) ya fadi a kaina abin da ya fadi a kan Ali ranar Tabuka, ("Ashe ba ka yarda ka kasance a gare ni kamar yadda Haruna ya kasance ga Musa ba, sai dai kawai babu Annabi a bayana"), shi ya fi soyuwa a gare ni sama da in mallaki abin da rana ta fito a kansa, lalle ba zan sake shiga gidanka matukar ina raye ba, sai yayi tafiyarsa(11). Ibn Athir ma ya ce: "Wata rana Bisr bn Arta'ah ya kasance a gidan Mu'awiyya sai ya fadi mummunar kalma a kan Imam Ali (a.s), nan take sai Zayd bn Umar bn al-Khattab da mahaifiyarsa Ummu Khultoom bint Ali suka buge shi da sanda har suka raunana shi(12)". Haka nan kuma ya nakalto cewa: "Lokacin da aka nada Mughira gwamnan Kufa, ya aike da Shihab zuwa garin Rayyu a matsayin mai kula da garin, alhali kuwa ya kasance mai yawaita zagin Ali a kan mimbari, kuma haka ya ci gaba da yi har lokacin da Ziyad ya karbi jagorancin garin Kufa(13)". "Wata rana Ziyad ya tara mutanen Kufa a fadarsa inda ya tilasta musu la'antar Ali, wanda kuwa ya kiya, sai ya kashe shi". Wannan yanayi na zagin Aliyu bn Abi Talib (a.s) dai ya ci gaba har lokacin da Umar bn Abdul'Aziz ya dare karagar mulki, inda ya hana hakan da kuma yin kwaskwa-rima ga jami'an gwamnati. Al-Mas'udi ya ci gaba da cewa: "Umar dai ya kasance mutum mai tsantsaini da kaskantar da kai. Ya sallami jami'an gwamnatin Umayyawa wacce ta wuce da kuma sanya wasu wadanda suke na kirki, wadanda suke bin tafarkinsa na gudanar da al'amurra. Shi ne wanda ya kawo karshen la'antar Ali (a.s) da ake yi akan mimbarori, da maye gurbin hakan da wannan aya ta Alkur'ani mai girma: ( ربَّنا أغفرلنا ولإخواننا الذين سبقونا بالإيمان ولا تجعل في قلوبنا غلاًّ للذين أمنوا' ربّنا إنَّك غفور رحيم ) "Ya Ubangijinmu! Ka yi mana gafara da kuma 'yan'uwanmu, wadanda suka riga mu yin imani, kada Ka sanya wani kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jin kai".(Suratul Hashr: 59:10). Wasu kuma suka ce wannan ayar ce ya sanya maimakon la'antar da ake wa Ali (a.s): ( إنّ الله يأْمر بالعدل والإحسان وايتاء ذي القربى وينهى عن الفحشاء والمنكر والبغي ) "Lalle Allah na yin umurni da adalci da kyautatawa, da bai wa ma'abucin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka ki da rarrabe jama'a...". (Suratun Nahl: 16:90). Wasu kuma suka ce dukkan biyun ne ya sanya, kuma al'umma suka ci gaba da amfani da su a hudubobi har zuwa yau(14)". Idan muka bar dalilan da suka rurata wutan wannan yunkuri da kuma karfin 'yan adawa, da suke kira ga gudanar da hukumce-hukumcen adalci da daidaitawa tsakanin al'umma da Musulunci ya ke kira zuwa gare shi, da girmama nufin al'umma da kuma riko da koyarwa da kuma akidun Musulunci wajen mu'amala ta siyasa da sauran al'umma. Haka nan kuma idan muka rufe ido kan hakan, muka kuma yi darasin yanayin tattalin arziki na wancan lokacin da kuma yadda mahukuntan suka yi karen tsaye wa tsarin rabon tattalin arziki na Musulunci wanda yake kira zuwa ga daidaituwa wajen rarraba dukiya, haramcin boye kayayyaki, wajibcin daukan nauyi da biyan bukatun marasa galihu, bugu da kari kan matsaloli na tsaro, to za mu ga cewa duk wadannan abubuwa sun kasance dalilai masu karfi na motsa zukatan al'umma da kuma matsowa kusa ga Imam Husaini (a.s) don jagorantarsu wajen kawar da irin wannan tsari. Hakika marasa galihu daga cikin al'umma sun fara kosawa da yadda ake take hakkokinsu da kuma irin tsananin talauci da suke fama da shi, a gefe guda kuma wasu 'yan tsiraru suna wasa da dukiyoyinsu, duk kuwa da cewa Allah Madaukakin Sarki Ya yi tsokaci kan hakan: ( والَّذِينَ يَكْنزون الذَّهَبَ والفِضةَ ولا يُنْفِقُونها في سبيلِ اللهِ فَبَشِّرهُمْ بِعَذابٍ أليمٍ ) "Kuma wadanda suke taskacewar zinariya da azurfa, kuma ba su ciyar da ita a cikin hanyar Allah, to, ka yi musu bushara da azaba mai radadi". (Suratul Tauba: 9:34). ما أفاءَ اللهُ على رسولِهِ من أهْلِ القرى فلِلَّهِ وللرَّسُولِ ولِذي القُربى واليَتامى والمَسَاكِين وابنِ السَّبيلِ كَي لايكونَ دولةً بينَ الأغْنياءِ منْكمْ وما اتَاكُم الرَّسولَُ فخُذوهُ وما نهاكمْ غنهُ فانتَهوا واتَّقُوا اللهَ إنَّ اللهَ شَديدُ الْعِقَابِ "Abin da Allah Ya sanya shi ganima ga ManzonSa daga mutanen kauyukan nan, to, na, Allah ne, kuma na ManzonSa ne, kuma na masu dangantaka da maraya da miskinai da dan hanya (matafiyi) ne, domin kada ya kasance abin shawagi a tsakanin mawadata daga cikinku, kuma abin da Manzo ya ba ku, to, ku kama shi, kuma abin da ya hane ku, to, ku bar shi. Kuma ku bi Allah da takawa. Lalle Allah, Mai tsananin ukuba ne". . (Suratul Hashri: 59:7). Hakika tarihi ya siffanta mana yadda yanayin tattalin arziki da kuma raba shi tsakanin al'umma ya kasance a wancan lokacin, wasu 'yan tsiraru ne suka mallake dimbin arzikin al'umma. A matsayin misali, tarihin ya bayyana mana sunayen wasu mutane wadanda suka wawuri dukiyoyin al'umma saboda alakar da suke da ita da gidan sarautar Umayyawa tun daga lokacin 'Shiryayyun Halifofi' har zuwa lokacin mulkin Yazid. Malaman tarihin sun bayyana cewa: 'Amru bn al-Aas, gwamnan Masar a lokacin Mu'awiyya, ya mallaki kadda-rorin da suka kai kimanin dinare dubu dari uku da ashirin da biyar, dirhami dubu, kayayyakin gona da suka kai dinare dubu dari biyu a Masar da kuma sanannen makeken ginin nan da ake ce al-Waht da aka kiyasta kudinsa kimanin dirhami dubu goma'. 'Haka nan kuma Abdurrahman bn Awf ya kasa gadonsa gida goma sha shida ga matayensa, inda kowace guda ta sami dirhami dubu tamanin(15)'. "Marwan bn Hakam ya kwashi kimanin dinare dubu dari biyar na kudaden shigan da aka kawo daga Afirka(16)". "Ibn al-Aas ya karbi kyautar da ta kai kimanin dirhami dubu dari(17)". "Kamar yadda Abdullah bn Khalid bn Asid ya karbi wata kyauta da ta kai kimanin dirhami dubu dari hudu(18)". "An kiyasta dukiyar Ya'ali bn Umayyah ta kai dinare dubu dari biyar, ban da basussukan da ya ke bin mutane da kuma sauran kaddarori da suka kai dinare dubu dari uku(19)". "Sa'ad bn Abi Wakkas, a lokacin mutuwarsa, ya bar kimanin dirhami dubu dari biyu da hamsin(20)". "Sa'id bn al-Musayyab ya nakalto cewa Zaid bn Thabit ya bar zinare da arzurfan da sai da gatari ake saransu da kuma dukiya da kaddarar da ta kai kimanin dinare dubu dari lokacin a lokacin mutuwarsa(21)". Wannan kadan kenan daga cikin abin da tarihi ya nakalto mana kan abubuwan da suka faru, ko da yake lamarin ba wai kawai ya takaita ba ne ga wadannan mutane da aka ambata, face dai kawai misali ne na irin mummunan yanayi na tattalin arziki da wasa da kudaden al'umma da aka yi. Wannan yanayi da ya kasa al'ummar musulmi zuwa kashi biyu, kashin fakirai marasa galihu da kuma kashin masu abin hannu wadanda suke ci da gumin al'umma, lamarin da ya saba wa tsarin Musulunci da ya yi kira zuwa ga daidaituwa tsakanin al'umma da kuma haramta satan kudaden al'umma da mallaka su ga wadansu kashi na al'ummar. Don haka irin wannan mummunan yanayi na tattalin arziki da al'umma suka shiga na daga cikin dalilan da suka motsa wutar wannan yunkuri, ta yadda kashin marasa galihu wadanda ake zalunta da kuma masu kira zuwa ga daidaito suka koma bangaren Imam Husaini (a.s), a matsayinsa na mutum guda wanda kawai zai iya gudanar da shari'a da kuma dokokin Musulunci kamar yadda ake yi a lokacin rayuwar Ma'aikin Allah (s.a.w.a). ____________ (1)- Maktal al-Husaini na al-Khawarizmi, juzu'i na 1, shafi na 88. (2)- Maktal al-Husaini na Ibn Dawus, shafi na 11. (3)- Al-Irshad na Shaikh al-Mufid, shafi na 204. (4)- Maktal al-Husain na Abdurrazak al-Mukarram, shafi na 141 da kuma na 142. (5)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi na 320 da Tarikh al-Umam wa al-Muluk na Tabari, juzu'i na 7, shafi na 104. (6)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi na 328. (7)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi na 338, ya nakalto daga Bihar al-Anwar na Allamah Majlisi, juzu'i na 10, shafi na 149. (8)- Sulhu al-Hasan na Shaikh Radhi Al' Yasin, shafi 328. (9)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 3, shafi na 462. (10)- Kamar na sama. (11)- Muruj al-Zahab na al-Mas'udi, juzu'i na 3, shafi na 14. (12)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 4, shafi na 12. (13)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 3, shafi na 413. (14)- Muruj al-Zahab na al-Mas'udi, juzu'i na 3, shafi na 183 da 184. (15)- Kamar na sama, shafi na 23. (16)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 3, shafi na 91. (17)- Al-Ma'arif na Ibn Kutaibah al-Dinuri, shafi na 84. (18)- Kamar na sama. (19)- Muruj al-Zahab na al-Mas'udi, juzu'i na 2, shafi na 333. (20)- Dabakat na Ibn Sa'ad, juzu' i na 3, shafi na 105. (21)- Al-Kamil fi al-Tarikh na Ibn Athir, juzu'i na 2, shafi na 333.
http://www.5five-stars.com.ng/2019/09/dalilan-yunkurin-imam-husaini-as.html
0 notes
isiyasy · 5 years
Text
Sakon Jagoran Juyin Musulunci Ga Mahajjatan Bana
Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai Godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai tsira da amincin Allah su tabbata ga manzonsa amintacce, Muhammad cikamakin annabawa, da alayensa tsarkaka musamman hujjar Allah a bayan kasa, da sahabbansa da wadanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa ranar kiyama. Taron aikin hajji wanda ake gudanawa a kowace shekara, wata rahama ce ta ubangiji ga al’ummar musulmi. Kira ne a cikin kur’ani (ka yi kira a cikin mutane zuwa ga hajji) kira ne zuwa ga kowa wanda ya wanzu tsawon tarihi domin isa ga wannan rahama ta ubangiji, domin zukata da rayuka masu kaunar ubangiji su samu rabo daga wannan babbar albarka. A kowace shekara akwai darussa da ake samu daga aikin hajji, ta hanyar wasu daga cikin mutane ne kuma wadannan darussa da sakonni suke isa ga sauran al’ummar musulmi na duniya. Acikin aikin hajji akwai ambaton Allah da ibada, wanda shi ne ginshiki na asali wajen tarbiyya da daukakar mutum da kuma al’umma. Taro da haduwa a wuri guda alama ce da ke nuni da kasantuwar musulmi al’umma ce guda, haka nan kuma dukkanin motsi da kai-komo a cikin aikin hajji alama ce ta tauhidi. Dukkanin mahajjata suna yin komai tare, iri daya babu banbanci tsakanin mutane, dukkanin wadannan abubuwa ne da suke yin nuni a takaice da hakikanin al’ummar musulmi. Kowane Ihrami da dawafi da sa’ayi da tsayuwa da jifa da motsi da zama a cikin aikin hajji, isahara ce zuwa ga wata taswira ta hakikanin musulunci. Musayar bayanai da abubuwan da suke faruwaa tsakanin mutanen kasashe da yankuna masu nisa da juna, bayyana mahanga da masaniya da kuma samun labaran juna, da kawar da rashin fahimta, da kusanto da zukata, da samun fadaka kan makiya na bai daya, wannan babban sakamako ne na taron aikin hajji, wanda ba za a iya samun sa ta hanyar gudanar da daruruwan taruka a duniya ba. Nuna barranta, wato nuna kin amincewa da duk wani nau’in rashin tausayi da zalunci da munanan ayyuka na barna na azzaluman shugabanni na kowane zamani, da kuma yin turjiya a gaban zaluncin masu girman kai, hakan na daya daga cikin manyan lamurra masu albarka na aikin hajji, kuma hakan dama ce ga al’ummomin musulmi da ake zaunta. A yau kubuta daga tungar shirka da kafircin masu girman kai wanda Amurka ce a gaba, hakan na nufin barranta ne daga kisan wadanda ake zalunta da siyasar neman yaki a duniya, yin tir da kungiyoyin ta’addanci irin su Daesh da Balack Water ta kasar Amurka, nuna rashin amincewar al’ummar musulmi da haramtacciyar gwamnatin yahudawan sahyuniya masu kisan kananan yara da masu mara musu baya da kuma masuba su taimako, yin tir da siyasar Amurka da kawayenta da ke haddasa yake-yake a cikin yankin yammacin Asia da arewacin Afrika wanda ya jefa al’ummomi cikin matsananciyar wahala da musibu masu muni, yin tir da nuna wariya bisa bangaranci na yanki ko launin fata, yin tir da duk wasu munanan halaye na manyan masu girman kai da shishshigi da haifar da fitina wadanda suke kira zuwa gare su, sabanin kyawawan halaye madaukaka da kuma adalci da musulunci yake yin kira zuwa gare su. Wadannan kadan ne daga cikin tarin albarkar hajji irin na annabi Ibrahim wanda musulunci ya kiraye zuwa gare shi, wannan wani babban bangare ne mai muhimmanci daga cikin manyan gishikai da al’ummar musulmi ta kafu a kansu, a kowace shekara wasu daga cikin musulmi suna tafiya aikin hajji, wannan aiki da yake a matsayin wani taro mai girma da yake cike da ma’anoni, wanda yake yin ishara da kuma kira gare mu baki daya da mu zama irin wannan jama’a da taru a wuri guda domin wannan aiki mai girma. Masana na duniyar musulmi wadanda wasu daga cikinsu daga kasashe daban-daban suna halartar aikin hajji a halin yanzu, suna da babban nauyi da ya rataya a kansu. Wadannan darussa na hajji dole ne a isar da su zuwa ga sauran al’ummomi ta hanyar himma da kokarin masana, a isar musu da sakonni da ilimi da mahanga da zaburarwa da kuma gogewa da fadakarwa irin ta al’ummar musulmi da ke tattare da wannan aiki. A yau daya daga cikin batutuwa mafi muhimmanci ga al’ummar musulmi shi ne batun Falastinu, wanda yake a kan gaba a dukkanin batutuwa na siyasar duniyar musulmi, a dukkanin mazhabobinsu da kabilunsu da harsunansu. Zalunci mafi girma a cikin karnonin baya-bayan nan ya auku ne a Falastinu. A wannan abin da ya faru, dukkanin abin da al’umma guda take da shi, da ya hada da kasarta, gidajenta, gonakinta, arzikinta da kaddarori, alfarmarta, asalinta, duka an kwace. Wannan al’umma tare da taimakon ubangiji ba ta karaya ba, ba ta mika wuya ba, a yau tafi yadda take a jiya, ta fuskar turjiya da jarunta a fagen daga, amma kaiwa ga sakamakon da take bukata, yana bukatar taimakon dukkanin musulmi. Makircin da ake kira yarjejeniyar karni, Amurka azzaluma da kawayenta masu cin amana suna shirin aiwatar da shi, wannan babban laifi ne a kan dukkanin’yan adam, ba al’ummar Falastinu kawai ba. Muna kiran kowa wajen fitowa gaba-gaba domin rusa wannan makirci na makiya, da karfin Allah da ikonsa mun san cewa wannan makirci da ma wasu makirce-makircen na masu girman kai, za su rushe a gaban himma da imanin tungar gwagwarmaya. Allah mabuwayi yana cewa: (( Shin suna nufin wani kaidi ne? to, wadanda suka kafirta su ne wadanda ake yi wa kaidi.)) Allah mai girma da daukaka ya yi gaskiya. Ina rokon Allah da ya yi wa dukkanin alhazai gamo da katar da jinkai da lafiya, ya karbi ayyukansu na ibada. Sayyid Ali Kahmenei 3Zulhijjah 1440-5/8/2019
from Blogger https://ift.tt/2GXYcnC
0 notes
isiyasy · 5 years
Quote
Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai Godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai tsira da amincin Allah su tabbata ga manzonsa amintacce, Muhammad cikamakin annabawa, da alayensa tsarkaka musamman hujjar Allah a bayan kasa, da sahabbansa da wadanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa ranar kiyama. Taron aikin hajji wanda ake gudanawa a kowace shekara, wata rahama ce ta ubangiji ga al’ummar musulmi. Kira ne a cikin kur’ani (ka yi kira a cikin mutane zuwa ga hajji) kira ne zuwa ga kowa wanda ya wanzu tsawon tarihi domin isa ga wannan rahama ta ubangiji, domin zukata da rayuka masu kaunar ubangiji su samu rabo daga wannan babbar albarka. A kowace shekara akwai darussa da ake samu daga aikin hajji, ta hanyar wasu daga cikin mutane ne kuma wadannan darussa da sakonni suke isa ga sauran al’ummar musulmi na duniya. Acikin aikin hajji akwai ambaton Allah da ibada, wanda shi ne ginshiki na asali wajen tarbiyya da daukakar mutum da kuma al’umma. Taro da haduwa a wuri guda alama ce da ke nuni da kasantuwar musulmi al’umma ce guda, haka nan kuma dukkanin motsi da kai-komo a cikin aikin hajji alama ce ta tauhidi. Dukkanin mahajjata suna yin komai tare, iri daya babu banbanci tsakanin mutane, dukkanin wadannan abubuwa ne da suke yin nuni a takaice da hakikanin al’ummar musulmi. Kowane Ihrami da dawafi da sa’ayi da tsayuwa da jifa da motsi da zama a cikin aikin hajji, isahara ce zuwa ga wata taswira ta hakikanin musulunci. Musayar bayanai da abubuwan da suke faruwaa tsakanin mutanen kasashe da yankuna masu nisa da juna, bayyana mahanga da masaniya da kuma samun labaran juna, da kawar da rashin fahimta, da kusanto da zukata, da samun fadaka kan makiya na bai daya, wannan babban sakamako ne na taron aikin hajji, wanda ba za a iya samun sa ta hanyar gudanar da daruruwan taruka a duniya ba. Nuna barranta, wato nuna kin amincewa da duk wani nau’in rashin tausayi da zalunci da munanan ayyuka na barna na azzaluman shugabanni na kowane zamani, da kuma yin turjiya a gaban zaluncin masu girman kai, hakan na daya daga cikin manyan lamurra masu albarka na aikin hajji, kuma hakan dama ce ga al’ummomin musulmi da ake zaunta. A yau kubuta daga tungar shirka da kafircin masu girman kai wanda Amurka ce a gaba, hakan na nufin barranta ne daga kisan wadanda ake zalunta da siyasar neman yaki a duniya, yin tir da kungiyoyin ta’addanci irin su Daesh da Balack Water ta kasar Amurka, nuna rashin amincewar al’ummar musulmi da haramtacciyar gwamnatin yahudawan sahyuniya masu kisan kananan yara da masu mara musu baya da kuma masuba su taimako, yin tir da siyasar Amurka da kawayenta da ke haddasa yake-yake a cikin yankin yammacin Asia da arewacin Afrika wanda ya jefa al’ummomi cikin matsananciyar wahala da musibu masu muni, yin tir da nuna wariya bisa bangaranci na yanki ko launin fata, yin tir da duk wasu munanan halaye na manyan masu girman kai da shishshigi da haifar da fitina wadanda suke kira zuwa gare su, sabanin kyawawan halaye madaukaka da kuma adalci da musulunci yake yin kira zuwa gare su. Wadannan kadan ne daga cikin tarin albarkar hajji irin na annabi Ibrahim wanda musulunci ya kiraye zuwa gare shi, wannan wani babban bangare ne mai muhimmanci daga cikin manyan gishikai da al’ummar musulmi ta kafu a kansu, a kowace shekara wasu daga cikin musulmi suna tafiya aikin hajji, wannan aiki da yake a matsayin wani taro mai girma da yake cike da ma’anoni, wanda yake yin ishara da kuma kira gare mu baki daya da mu zama irin wannan jama’a da taru a wuri guda domin wannan aiki mai girma. Masana na duniyar musulmi wadanda wasu daga cikinsu daga kasashe daban-daban suna halartar aikin hajji a halin yanzu, suna da babban nauyi da ya rataya a kansu. Wadannan darussa na hajji dole ne a isar da su zuwa ga sauran al’ummomi ta hanyar himma da kokarin masana, a isar musu da sakonni da ilimi da mahanga da zaburarwa da kuma gogewa da fadakarwa irin ta al’ummar musulmi da ke tattare da wannan aiki. A yau daya daga cikin batutuwa mafi muhimmanci ga al’ummar musulmi shi ne batun Falastinu, wanda yake a kan gaba a dukkanin batutuwa na siyasar duniyar musulmi, a dukkanin mazhabobinsu da kabilunsu da harsunansu. Zalunci mafi girma a cikin karnonin baya-bayan nan ya auku ne a Falastinu. A wannan abin da ya faru, dukkanin abin da al’umma guda take da shi, da ya hada da kasarta, gidajenta, gonakinta, arzikinta da kaddarori, alfarmarta, asalinta, duka an kwace. Wannan al’umma tare da taimakon ubangiji ba ta karaya ba, ba ta mika wuya ba, a yau tafi yadda take a jiya, ta fuskar turjiya da jarunta a fagen daga, amma kaiwa ga sakamakon da take bukata, yana bukatar taimakon dukkanin musulmi. Makircin da ake kira yarjejeniyar karni, Amurka azzaluma da kawayenta masu cin amana suna shirin aiwatar da shi, wannan babban laifi ne a kan dukkanin’yan adam, ba al’ummar Falastinu kawai ba. Muna kiran kowa wajen fitowa gaba-gaba domin rusa wannan makirci na makiya, da karfin Allah da ikonsa mun san cewa wannan makirci da ma wasu makirce-makircen na masu girman kai, za su rushe a gaban himma da imanin tungar gwagwarmaya. Allah mabuwayi yana cewa: (( Shin suna nufin wani kaidi ne? to, wadanda suka kafirta su ne wadanda ake yi wa kaidi.)) Allah mai girma da daukaka ya yi gaskiya. Ina rokon Allah da ya yi wa dukkanin alhazai gamo da katar da jinkai da lafiya, ya karbi ayyukansu na ibada. Sayyid Ali Kahmenei 3Zulhijjah 1440-5/8/2019
http://isiyasy.blogspot.com/2019/08/sakon-jagoran-juyin-musulunci-ga.html
0 notes
isiyasy · 5 years
Quote
Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai Godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai tsira da amincin Allah su tabbata ga manzonsa amintacce, Muhammad cikamakin annabawa, da alayensa tsarkaka musamman hujjar Allah a bayan kasa, da sahabbansa da wadanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa ranar kiyama. Taron aikin hajji wanda ake gudanawa a kowace shekara, wata rahama ce ta ubangiji ga al’ummar musulmi. Kira ne a cikin kur’ani (ka yi kira a cikin mutane zuwa ga hajji) kira ne zuwa ga kowa wanda ya wanzu tsawon tarihi domin isa ga wannan rahama ta ubangiji, domin zukata da rayuka masu kaunar ubangiji su samu rabo daga wannan babbar albarka. A kowace shekara akwai darussa da ake samu daga aikin hajji, ta hanyar wasu daga cikin mutane ne kuma wadannan darussa da sakonni suke isa ga sauran al’ummar musulmi na duniya. Acikin aikin hajji akwai ambaton Allah da ibada, wanda shi ne ginshiki na asali wajen tarbiyya da daukakar mutum da kuma al’umma. Taro da haduwa a wuri guda alama ce da ke nuni da kasantuwar musulmi al’umma ce guda, haka nan kuma dukkanin motsi da kai-komo a cikin aikin hajji alama ce ta tauhidi. Dukkanin mahajjata suna yin komai tare, iri daya babu banbanci tsakanin mutane, dukkanin wadannan abubuwa ne da suke yin nuni a takaice da hakikanin al’ummar musulmi. Kowane Ihrami da dawafi da sa’ayi da tsayuwa da jifa da motsi da zama a cikin aikin hajji, isahara ce zuwa ga wata taswira ta hakikanin musulunci. Musayar bayanai da abubuwan da suke faruwaa tsakanin mutanen kasashe da yankuna masu nisa da juna, bayyana mahanga da masaniya da kuma samun labaran juna, da kawar da rashin fahimta, da kusanto da zukata, da samun fadaka kan makiya na bai daya, wannan babban sakamako ne na taron aikin hajji, wanda ba za a iya samun sa ta hanyar gudanar da daruruwan taruka a duniya ba. Nuna barranta, wato nuna kin amincewa da duk wani nau’in rashin tausayi da zalunci da munanan ayyuka na barna na azzaluman shugabanni na kowane zamani, da kuma yin turjiya a gaban zaluncin masu girman kai, hakan na daya daga cikin manyan lamurra masu albarka na aikin hajji, kuma hakan dama ce ga al’ummomin musulmi da ake zaunta. A yau kubuta daga tungar shirka da kafircin masu girman kai wanda Amurka ce a gaba, hakan na nufin barranta ne daga kisan wadanda ake zalunta da siyasar neman yaki a duniya, yin tir da kungiyoyin ta’addanci irin su Daesh da Balack Water ta kasar Amurka, nuna rashin amincewar al’ummar musulmi da haramtacciyar gwamnatin yahudawan sahyuniya masu kisan kananan yara da masu mara musu baya da kuma masuba su taimako, yin tir da siyasar Amurka da kawayenta da ke haddasa yake-yake a cikin yankin yammacin Asia da arewacin Afrika wanda ya jefa al’ummomi cikin matsananciyar wahala da musibu masu muni, yin tir da nuna wariya bisa bangaranci na yanki ko launin fata, yin tir da duk wasu munanan halaye na manyan masu girman kai da shishshigi da haifar da fitina wadanda suke kira zuwa gare su, sabanin kyawawan halaye madaukaka da kuma adalci da musulunci yake yin kira zuwa gare su. Wadannan kadan ne daga cikin tarin albarkar hajji irin na annabi Ibrahim wanda musulunci ya kiraye zuwa gare shi, wannan wani babban bangare ne mai muhimmanci daga cikin manyan gishikai da al’ummar musulmi ta kafu a kansu, a kowace shekara wasu daga cikin musulmi suna tafiya aikin hajji, wannan aiki da yake a matsayin wani taro mai girma da yake cike da ma’anoni, wanda yake yin ishara da kuma kira gare mu baki daya da mu zama irin wannan jama’a da taru a wuri guda domin wannan aiki mai girma. Masana na duniyar musulmi wadanda wasu daga cikinsu daga kasashe daban-daban suna halartar aikin hajji a halin yanzu, suna da babban nauyi da ya rataya a kansu. Wadannan darussa na hajji dole ne a isar da su zuwa ga sauran al’ummomi ta hanyar himma da kokarin masana, a isar musu da sakonni da ilimi da mahanga da zaburarwa da kuma gogewa da fadakarwa irin ta al’ummar musulmi da ke tattare da wannan aiki. A yau daya daga cikin batutuwa mafi muhimmanci ga al’ummar musulmi shi ne batun Falastinu, wanda yake a kan gaba a dukkanin batutuwa na siyasar duniyar musulmi, a dukkanin mazhabobinsu da kabilunsu da harsunansu. Zalunci mafi girma a cikin karnonin baya-bayan nan ya auku ne a Falastinu. A wannan abin da ya faru, dukkanin abin da al’umma guda take da shi, da ya hada da kasarta, gidajenta, gonakinta, arzikinta da kaddarori, alfarmarta, asalinta, duka an kwace. Wannan al’umma tare da taimakon ubangiji ba ta karaya ba, ba ta mika wuya ba, a yau tafi yadda take a jiya, ta fuskar turjiya da jarunta a fagen daga, amma kaiwa ga sakamakon da take bukata, yana bukatar taimakon dukkanin musulmi. Makircin da ake kira yarjejeniyar karni, Amurka azzaluma da kawayenta masu cin amana suna shirin aiwatar da shi, wannan babban laifi ne a kan dukkanin’yan adam, ba al’ummar Falastinu kawai ba. Muna kiran kowa wajen fitowa gaba-gaba domin rusa wannan makirci na makiya, da karfin Allah da ikonsa mun san cewa wannan makirci da ma wasu makirce-makircen na masu girman kai, za su rushe a gaban himma da imanin tungar gwagwarmaya. Allah mabuwayi yana cewa: (( Shin suna nufin wani kaidi ne? to, wadanda suka kafirta su ne wadanda ake yi wa kaidi.)) Allah mai girma da daukaka ya yi gaskiya. Ina rokon Allah da ya yi wa dukkanin alhazai gamo da katar da jinkai da lafiya, ya karbi ayyukansu na ibada. Sayyid Ali Kahmenei 3Zulhijjah 1440-5/8/2019
http://isiyasy.blogspot.com/2019/08/sakon-jagoran-juyin-musulunci-ga.html
0 notes
isiyasy · 5 years
Text
BAZA A IYA KAUCEWA ZANGA-ZANGAR JUYIN JUYA HALI BA A NIJERIYA
Domin zanga-zanga ce ta neman ayi adalci adaina zalunci  Na tabbata ba wani ɗan adam ma'abovin hankali dabyake son wanzuwar zalunci. bilhasali ma umarni ne na mahaliccin mu a tsayar da adalci a cikin al'umma wanda shine dalilin aiko Annabawa da Manzanni. Aikin da Imam Mahdi(A) zai ƙarƙare shi nan ba da daɗewa ba. Dukkan masu ƙyamar zalunci a ƙasarmu su shirya dan tarbar wannan loakvin in yazo na yin arangama a tsakanin masu son adalci da masu ƙaunar ayi zalunci.
Zanga zanga ce wacce an riga anyi mata key tun a 2017 a garin Abuja kumanhaka zata ci gaba da yardar Allah har ya zuwa ranar da lissafin wara aitan nasa....... ya cika, abune da ba makawa za a kori azzalumai daga mulkin Nigeria.
A ranar 19122017 na kasance a gidan ɗaya daga cikin ƴan siyasar ƙasarmu a Nigeriya da dare daga Kano a gidansa da yake a Abuja, Ni da wani abokina wanda sun daɗe tare dashi, ni kuwa wannan ne karon farko na haɗuwa ta dashi.
Acikin hirarrakin da mukayi da shi ya tambaye ni mahanga ta dangane da zaɓen 2019. Me nake hange zai faru. Naga yamansa cewa Maguɗi ta tashin hankali ne zasu kasance da zai tarwatsa kashin dankali da zai tarwatsa tsarin zalunci na rashin adalci na mahukuntar Nigeria. Na gaya masa cewa da yiwuwar Ƴan adawa zasu samu nasara saidai ba za ataɓa basu nasararsu ba, za ayi maguɗi ne. Na ƙara da cewa ina roƙon Allah ya sanya wannan maguɗin ya kasance. In ya kasance da yiwuwar samun juyin juya hali wanda lamarin zai faro daga ƴan kudanci Nigeria. Zanga-zanga ce da ba za aiya dakatar da ita ba. Na gaya masa Nigeria ba buƙatar mu shugaba ya kasance Musulmi bane ko Kirista Adali muke buƙata wanda shine kuma abin da muka rasa. Shima a nashi sharhin ya nuna cewa ya hango haka cewa da yiwuwar bafa za a dauwama a haka ba dole a samu sauyi na gaba ɗaya.
Alhamdulillah anyi zaɓe an gama kuma abin da mukayi hasashe na faruwar maguɗin zaɓe ya kasance. Yanzu sai marhala ta biyu da muke hasashen sa acikin lissafin 777 na gaya wa Mr Buhari ya haddace a cikin saƙon Giyar Mulki dana rubuta masa, dannzaiyi masa amfani. Ku biyo ni bashin rubutu akan adadin 777 In Allah yaso.
A rubutun Labarin Nijeriya a a cikin Alƙur'ani... da kuma na Wanene Zakzaky na ambata cewa da yiwuwar arangamar neman sauyi a Nigeria zai soma ne daga Kudancin Nigeria ko kuma daga ƴan Kudanci koda kuwa a Arewa suke da zama. 
Alahmdulillah sai gashi a cikar kwanaki 69 daga rantsar da sabuwar gwamnatin an aiyana ranar ta zama ranar shirya gangamin Zanga-zangar Juyin juya hali a faɗin Nigeria Sai dai bana ganin wannan yunƙurin zai yiwu a yanzu domin rashin kammaluwar muƙaddamomin Yunƙurin da kasan cewar Alƙalin da zai yanke hukunci akan lamarin bai kammala shirinsa ba. Amma dai Juyi ne da ba wani abin halitta da ya isa ya dakatar dashi, in ba Allah ba. Bana jin Allah zai dakatar da lamarin domin Allah yana son adalci kuma yayi umarni da ayi adalic a lokacin da yayi haramci ga aikata zalunci. Amma in har gwamnati maici sun sauya zuwa ga aikata adalci Allah na iya sauya lamarin ya wanzar dasu. Sai dai an ce girman kai rawanin tsiya. ƙyashi da hassada zasuyi masu tasiri mai yawa.
A rubutun da nayi a ranar 12032019 mai suna  HASASHE A CIKIN MULKIN SABON SARKIN  NIJERIYA NA 2019 ZUWA 2023
Na kawo hasashen Malam Huda akan wasu abubuwa da zasu faru a wannan gwamnatin na Next Level kuma ƴan satuttuka  daga zabe sai ga lamarin wasu sun fara faruwa a zahirance. Bari na ɗan tuna mana hasashen tare da ɗan yin sharhi a wasu nuƙuɗoɗin. In baku manta ba Malam Huda labari yake bani na hasashen da yake dashi na abubuwan da ya hango zasu iya faruwa a Nigeria daga 2019 zuwa 2023.
Sai Malam Huda yaci gaba dancewa:
To yanzu bari na koma zuwa ga amsa tambayarka na uku, da kake son sanin ko ya yanayin mulkin da kuma al'umma zasu kasance a cikin wannan wa'adin na mulki mafi tsauri da tsohon Janar zai gudanar. Hasashe ne kamar  guda goma sha uku.
Hakika kayi tambaya a cikin tsananin shauƙin sanin amsar yanda rayuwa zata kasance. Cikar burin Sabon Sarki da masu zaɓensa, abu ne da kamar yuwa da suke da buƙatar tambayoyi, irin waɗannan Tanadin nasa zasu kawo ƙuncin rayuwa na wucin gadi. Cikar burin ƴan ƙasa ya ta’allaka da cakuɗewar al’amura(Hargitsi, zanga-zanga), Sabon sarki da masu naɗinsa, rayuwar ku cike ta ke da ababen kasada  na banmamaki.
Dangane da tattalin arziki kuwa. A mulkin Za a tara kuɗaɗe masu yawa. Za a tara su a sirrance da zummar yin aiki. A irin wannan naɗin na ɗauki ɗora, yanayin cikar burin tara dukiya ko more rayuwa, abu ne da zai yi hawalar yiwuwa.
A cikin ƴan'uwa na Harkar Musulunci kuwa, da yiwuwar samun yaɗuwar labaran ƙarya ko na cutarwa ta hanyar rubuce-rubuce ta kafafen sada zumunta, da yaɗa labarai, tsegunguma da labaran ƙanzon Kurege ko annamimanci ko ince na ɓata suna  daga Makusanta, ('yan shi'ar da gwamnati ta yarda dasu) tarkon makircin da aka shirya  ga yanayin zamantakewar al'umma zasu baiyana, jajircewar tabbatar hadafi  yana iya jinkirtad da  duk shirin makiya.
( Ya kamata ace ƴan'uwa tun ba yau ba sunyi la'akari da wannan shasashen da ya gabata  dan asan abinyi kar aba maƙiya kafa, jajircewa babyana nufin tsaurin kai bane. Bin hanyoyin hikima ne dan tunkuɗewar hadafin maƙiya. Yaɗaɗɗun labarai daka hasaso akan mayar da sune  ta hanya hikima, "Kayi kira zuwa ga hanyar Ubangijin ka da hikima da wa'azi kyakkyawa" ) Iyaye su sani, rayuwar iyali mai cike da rashin walwala, rashin cikakken ƴanci saboda rashin kasancewar tsofaffin iyaye,(masu shiryarwa), rashe-rashe ko lalacewar dukiya, wariya, kaɗaici. duk zasu addabi al'umma.
Dangane da Yaran sabon sarki kuwa, a zamanin Sabon Sarkin  na 2019 zai fuskanci cutarwa a soyayya, sabon Sarki zaka samu haka ne daga wanda ka ke so, cin amana daga ɗaya daga cikin yaranka Ko kuma wani abu na kaucewa shari’a daga ɓangaren abin da zai sanya a yi hukunci (sata ko zamba) yafi dacewa a zauna a kula da gida. (
Office) Kasar (Nijeriya) zata yi rashin lafiya. Domin rashin aikinyi ko ci baya a mukami (daga babban matsayi zuwa ƙarami),  watau da yiwuwar za a rage ma'ikata. Hakan cuta ne mai ciwo mai wahalar magani, in haka ya kasance to anyi matukar lalata jurewar cututtukan halittu(al'ummar ƙasar).
Da yiwuwar Mata (Ko kuma gwamnatocin jahohi) a Ƙasar zasu zama masu son Zaman lafiya da kuma gaskiya a zamantakewar aure( ko kuma ga al'ummar da suke mulka), amma da yiwuwar samun karancin sha’awa, zasu rika gyara rikicin aurensu a  cikin lumana.
Ina sake nanata maka cewa; Kayi tambaya cikin tsananin zaƙuwar sanin amsar yanda rayuwa zata kasance a sabon salon mulkin tsohon janar mai tsanani. Kasani cewa; Cikar burin Sabon Sarki abu ne da kamar yuwa da suke da buƙatar tambaya, irin waɗannan Tanadin na sa sazu kawo kuncin rayuwa na wucin gadi. Cikar burin Ƴan ƙasa ya ta’allaƙa da cakuɗewar al’amura (Hargitsi, zanga-zanga), Sabon sarki da masu naɗinsa, ina jadda maku cewa; rayuwar ku cike ta ke da ababen kasada  na ban mamaki.
Akwai Barazanar haɗari  a cikin wannan yanayin tafiyar mulkin na watanni 48. Malam Ra'is ka  sani zaka iya  tsintar kanka  a Ƙasar da ake juyin mulki na juyin juya hali, ko zanga-zanga masu munin gaske.
(Sansomin yunƙurin wannan hasashen ne ya firgita gwamnatin Next Level a wannan satin har dabyin awon gaba da madugun shiryawan. Kash! wannan wani gangami ne danzai yi wahalar a kawar da shi daga ruhin mutane ma'aboda ƙyamar zalunci, domin ba wani mai son adalci da ba zaiyi marhabin da wannan yinurin ba, duk da cewa a yanzu barazanace kawai, magasgancin yana nan tafe a bazatance.)
Ka gaya wa Sabon Sarki; cin nasara na buƙatar yin aiki ne a kowane lokaci da kuma neman cikar burika, ana buƙatar tsananin juriya wajen cimma hadafi. Sai dai wannan a baiyane yake, ya Sabon Sarki ka dogara ne da wasu wajen cikar burika, maimakon matsayinka.
Cin sa'a ko Cikar burinku zai zo a lokacin da Rabuwa da aboki na kwarai ya kasance, abokan sabon sarki suka koma maƙiya, kasani cewa da akwai hadari akan rashin tantancewar al'amuran da zasu bijiro anan gaba kaɗan.
(Wannan hasashen abin lura ne sosai ga ƴan'uwa dan naga har ana neman gaza tantancewar  a loakcin fuskantar haɗari. Mu kula sosai domin masoyan sabon sarki na gab  da su zame masa maƙiya)
Kasarku da yiwuwar zata zama tamkar Kurkuku, domin Cututtukanta  boyayyu da sannu zasu yi ta baiyana. Ya Ra'is ka shirya dan zaka sha mamaki, domin ana biye da shi. Zuwa Asibiti domin neman lafiya, kayi kallo da idon basira zai rage raɗaɗin wahalhalun ko nace maka ruɗani.
(A wannan hasashen lamari ne danya sashafi Saiyid Zakzaky da kuma wani daga Azzaluman Nijeriya, Da wannannne muƙaddama zata kammala da yardar Allah. A lokacin da aka kammala watanni 63 na wahalhalu daga waƙi'ar Ƙudus na 2014 a ranar 28/12/1440 )
Zumudi yana taka muhimmiyar rawa a kan yin tambaya. Jama'a zasu shaida cewa; Wasu ƙasashen suna taka mihimmiyar rawa su ma(wajen kawo ruɗu a ƙasarku Nijeriya). Ya Ra'is ka sani basu masauki da rashin yin katabus zai kawo illata.
( Waɗannan ƙasashen da aka kawo a hasashen nan sune ƙasashen da suke da dangantaka da rundunar Sufiyaniyawa, Ƙasashe biyu ne Saudiya da Isra'ila. Domin an ruwaici cewa rundunar Sufyaniy runduna ce ta Yahudu da larabawa.)
Ku sanar da Alƙalin cewa; abubuwan da suka faru suka kuma wuce (na cutarwa, zubar da jini, rushe-rushe da yin maguɗin zaɓe) suna da tasiri  mai yawa wajen kawo gyara. Yana da muhimmanci ga alƙalin da ya  shigo cikin lamarin. Yanayi ne mai muhimmanci domin yin dukkan abin da ya dace nayin aiki mai farashi, domin shine  mutum ɗaya rak  da  zai iya magance komai na matsaloli a ƙasar.
Allah ne masani akan komai, namu hasashe ne daga ɗan abin da muka sani, zartarwa na Ubangiji ne, domin shi mai yawan ilimi da hikima ne.
Sai Malam Huda ya ɗaga hannu yayi addu'u nima na ɗaga tare dashi kamar haka:
Ya Allah ka gaggauta nuna mana wannan lokacin da wannan alƙalin zai yanke wa ƙasarmu da al'ummarta hukunci na adalci, domin kawo gyara da warwarewa matsalolin da suka addabi wannan ƙasar tamu mai albarka. Ya Allah ka bashi dukkan taimako da kulawarka a gareshi, ka baiwa al'ummarmu dama da ikon karɓar hukuncin da zai yanke akansu da ƙasar gabaki ɗaya.
Ka sanar da masu son ganin anyi adalci a ƙasarmu Nijeriya mai albarka, musulmai da kirista, harma da wanɗan da basu bin wani addini, su shirya domin an kusa nemansu zuwa ga muhimmin aiki. Allah kataimaki duk wani mai son ganin anyi adalci, ka basu juriya akan ganin tabbatara haka.
Muhammad Sani Ra'is, Funtua. +2347034595991 03121440 04082019
from Blogger https://ift.tt/2YQ8oIV
0 notes
isiyasy · 5 years
Quote
Domin zanga-zanga ce ta neman ayi adalci adaina zalunci  Na tabbata ba wani ɗan adam ma'abovin hankali dabyake son wanzuwar zalunci. bilhasali ma umarni ne na mahaliccin mu a tsayar da adalci a cikin al'umma wanda shine dalilin aiko Annabawa da Manzanni. Aikin da Imam Mahdi(A) zai ƙarƙare shi nan ba da daɗewa ba. Dukkan masu ƙyamar zalunci a ƙasarmu su shirya dan tarbar wannan loakvin in yazo na yin arangama a tsakanin masu son adalci da masu ƙaunar ayi zalunci. Zanga zanga ce wacce an riga anyi mata key tun a 2017 a garin Abuja kumanhaka zata ci gaba da yardar Allah har ya zuwa ranar da lissafin wara aitan nasa....... ya cika, abune da ba makawa za a kori azzalumai daga mulkin Nigeria. A ranar 19122017 na kasance a gidan ɗaya daga cikin ƴan siyasar ƙasarmu a Nigeriya da dare daga Kano a gidansa da yake a Abuja, Ni da wani abokina wanda sun daɗe tare dashi, ni kuwa wannan ne karon farko na haɗuwa ta dashi. Acikin hirarrakin da mukayi da shi ya tambaye ni mahanga ta dangane da zaɓen 2019. Me nake hange zai faru. Naga yamansa cewa Maguɗi ta tashin hankali ne zasu kasance da zai tarwatsa kashin dankali da zai tarwatsa tsarin zalunci na rashin adalci na mahukuntar Nigeria. Na gaya masa cewa da yiwuwar Ƴan adawa zasu samu nasara saidai ba za ataɓa basu nasararsu ba, za ayi maguɗi ne. Na ƙara da cewa ina roƙon Allah ya sanya wannan maguɗin ya kasance. In ya kasance da yiwuwar samun juyin juya hali wanda lamarin zai faro daga ƴan kudanci Nigeria. Zanga-zanga ce da ba za aiya dakatar da ita ba. Na gaya masa Nigeria ba buƙatar mu shugaba ya kasance Musulmi bane ko Kirista Adali muke buƙata wanda shine kuma abin da muka rasa. Shima a nashi sharhin ya nuna cewa ya hango haka cewa da yiwuwar bafa za a dauwama a haka ba dole a samu sauyi na gaba ɗaya. Alhamdulillah anyi zaɓe an gama kuma abin da mukayi hasashe na faruwar maguɗin zaɓe ya kasance. Yanzu sai marhala ta biyu da muke hasashen sa acikin lissafin 777 na gaya wa Mr Buhari ya haddace a cikin saƙon Giyar Mulki dana rubuta masa, dannzaiyi masa amfani. Ku biyo ni bashin rubutu akan adadin 777 In Allah yaso. A rubutun Labarin Nijeriya a a cikin Alƙur'ani... da kuma na Wanene Zakzaky na ambata cewa da yiwuwar arangamar neman sauyi a Nigeria zai soma ne daga Kudancin Nigeria ko kuma daga ƴan Kudanci koda kuwa a Arewa suke da zama.  Alahmdulillah sai gashi a cikar kwanaki 69 daga rantsar da sabuwar gwamnatin an aiyana ranar ta zama ranar shirya gangamin Zanga-zangar Juyin juya hali a faɗin Nigeria Sai dai bana ganin wannan yunƙurin zai yiwu a yanzu domin rashin kammaluwar muƙaddamomin Yunƙurin da kasan cewar Alƙalin da zai yanke hukunci akan lamarin bai kammala shirinsa ba. Amma dai Juyi ne da ba wani abin halitta da ya isa ya dakatar dashi, in ba Allah ba. Bana jin Allah zai dakatar da lamarin domin Allah yana son adalci kuma yayi umarni da ayi adalic a lokacin da yayi haramci ga aikata zalunci. Amma in har gwamnati maici sun sauya zuwa ga aikata adalci Allah na iya sauya lamarin ya wanzar dasu. Sai dai an ce girman kai rawanin tsiya. ƙyashi da hassada zasuyi masu tasiri mai yawa. A rubutun da nayi a ranar 12032019 mai suna  HASASHE A CIKIN MULKIN SABON SARKIN  NIJERIYA NA 2019 ZUWA 2023 Na kawo hasashen Malam Huda akan wasu abubuwa da zasu faru a wannan gwamnatin na Next Level kuma ƴan satuttuka  daga zabe sai ga lamarin wasu sun fara faruwa a zahirance. Bari na ɗan tuna mana hasashen tare da ɗan yin sharhi a wasu nuƙuɗoɗin. In baku manta ba Malam Huda labari yake bani na hasashen da yake dashi na abubuwan da ya hango zasu iya faruwa a Nigeria daga 2019 zuwa 2023. Sai Malam Huda yaci gaba dancewa: To yanzu bari na koma zuwa ga amsa tambayarka na uku, da kake son sanin ko ya yanayin mulkin da kuma al'umma zasu kasance a cikin wannan wa'adin na mulki mafi tsauri da tsohon Janar zai gudanar. Hasashe ne kamar  guda goma sha uku. Hakika kayi tambaya a cikin tsananin shauƙin sanin amsar yanda rayuwa zata kasance. Cikar burin Sabon Sarki da masu zaɓensa, abu ne da kamar yuwa da suke da buƙatar tambayoyi, irin waɗannan Tanadin nasa zasu kawo ƙuncin rayuwa na wucin gadi. Cikar burin ƴan ƙasa ya ta’allaka da cakuɗewar al’amura(Hargitsi, zanga-zanga), Sabon sarki da masu naɗinsa, rayuwar ku cike ta ke da ababen kasada  na banmamaki. Dangane da tattalin arziki kuwa. A mulkin Za a tara kuɗaɗe masu yawa. Za a tara su a sirrance da zummar yin aiki. A irin wannan naɗin na ɗauki ɗora, yanayin cikar burin tara dukiya ko more rayuwa, abu ne da zai yi hawalar yiwuwa. A cikin ƴan'uwa na Harkar Musulunci kuwa, da yiwuwar samun yaɗuwar labaran ƙarya ko na cutarwa ta hanyar rubuce-rubuce ta kafafen sada zumunta, da yaɗa labarai, tsegunguma da labaran ƙanzon Kurege ko annamimanci ko ince na ɓata suna  daga Makusanta, ('yan shi'ar da gwamnati ta yarda dasu) tarkon makircin da aka shirya  ga yanayin zamantakewar al'umma zasu baiyana, jajircewar tabbatar hadafi  yana iya jinkirtad da  duk shirin makiya. ( Ya kamata ace ƴan'uwa tun ba yau ba sunyi la'akari da wannan shasashen da ya gabata  dan asan abinyi kar aba maƙiya kafa, jajircewa babyana nufin tsaurin kai bane. Bin hanyoyin hikima ne dan tunkuɗewar hadafin maƙiya. Yaɗaɗɗun labarai daka hasaso akan mayar da sune  ta hanya hikima, "Kayi kira zuwa ga hanyar Ubangijin ka da hikima da wa'azi kyakkyawa" ) Iyaye su sani, rayuwar iyali mai cike da rashin walwala, rashin cikakken ƴanci saboda rashin kasancewar tsofaffin iyaye,(masu shiryarwa), rashe-rashe ko lalacewar dukiya, wariya, kaɗaici. duk zasu addabi al'umma. Dangane da Yaran sabon sarki kuwa, a zamanin Sabon Sarkin  na 2019 zai fuskanci cutarwa a soyayya, sabon Sarki zaka samu haka ne daga wanda ka ke so, cin amana daga ɗaya daga cikin yaranka Ko kuma wani abu na kaucewa shari’a daga ɓangaren abin da zai sanya a yi hukunci (sata ko zamba) yafi dacewa a zauna a kula da gida. ( Office) Kasar (Nijeriya) zata yi rashin lafiya. Domin rashin aikinyi ko ci baya a mukami (daga babban matsayi zuwa ƙarami),  watau da yiwuwar za a rage ma'ikata. Hakan cuta ne mai ciwo mai wahalar magani, in haka ya kasance to anyi matukar lalata jurewar cututtukan halittu(al'ummar ƙasar). Da yiwuwar Mata (Ko kuma gwamnatocin jahohi) a Ƙasar zasu zama masu son Zaman lafiya da kuma gaskiya a zamantakewar aure( ko kuma ga al'ummar da suke mulka), amma da yiwuwar samun karancin sha’awa, zasu rika gyara rikicin aurensu a  cikin lumana. Ina sake nanata maka cewa; Kayi tambaya cikin tsananin zaƙuwar sanin amsar yanda rayuwa zata kasance a sabon salon mulkin tsohon janar mai tsanani. Kasani cewa; Cikar burin Sabon Sarki abu ne da kamar yuwa da suke da buƙatar tambaya, irin waɗannan Tanadin na sa sazu kawo kuncin rayuwa na wucin gadi. Cikar burin Ƴan ƙasa ya ta’allaƙa da cakuɗewar al’amura (Hargitsi, zanga-zanga), Sabon sarki da masu naɗinsa, ina jadda maku cewa; rayuwar ku cike ta ke da ababen kasada  na ban mamaki. Akwai Barazanar haɗari  a cikin wannan yanayin tafiyar mulkin na watanni 48. Malam Ra'is ka  sani zaka iya  tsintar kanka  a Ƙasar da ake juyin mulki na juyin juya hali, ko zanga-zanga masu munin gaske. (Sansomin yunƙurin wannan hasashen ne ya firgita gwamnatin Next Level a wannan satin har dabyin awon gaba da madugun shiryawan. Kash! wannan wani gangami ne danzai yi wahalar a kawar da shi daga ruhin mutane ma'aboda ƙyamar zalunci, domin ba wani mai son adalci da ba zaiyi marhabin da wannan yinurin ba, duk da cewa a yanzu barazanace kawai, magasgancin yana nan tafe a bazatance.) Ka gaya wa Sabon Sarki; cin nasara na buƙatar yin aiki ne a kowane lokaci da kuma neman cikar burika, ana buƙatar tsananin juriya wajen cimma hadafi. Sai dai wannan a baiyane yake, ya Sabon Sarki ka dogara ne da wasu wajen cikar burika, maimakon matsayinka. Cin sa'a ko Cikar burinku zai zo a lokacin da Rabuwa da aboki na kwarai ya kasance, abokan sabon sarki suka koma maƙiya, kasani cewa da akwai hadari akan rashin tantancewar al'amuran da zasu bijiro anan gaba kaɗan. (Wannan hasashen abin lura ne sosai ga ƴan'uwa dan naga har ana neman gaza tantancewar  a loakcin fuskantar haɗari. Mu kula sosai domin masoyan sabon sarki na gab  da su zame masa maƙiya) Kasarku da yiwuwar zata zama tamkar Kurkuku, domin Cututtukanta  boyayyu da sannu zasu yi ta baiyana. Ya Ra'is ka shirya dan zaka sha mamaki, domin ana biye da shi. Zuwa Asibiti domin neman lafiya, kayi kallo da idon basira zai rage raɗaɗin wahalhalun ko nace maka ruɗani. (A wannan hasashen lamari ne danya sashafi Saiyid Zakzaky da kuma wani daga Azzaluman Nijeriya, Da wannannne muƙaddama zata kammala da yardar Allah. A lokacin da aka kammala watanni 63 na wahalhalu daga waƙi'ar Ƙudus na 2014 a ranar 28/12/1440 ) Zumudi yana taka muhimmiyar rawa a kan yin tambaya. Jama'a zasu shaida cewa; Wasu ƙasashen suna taka mihimmiyar rawa su ma(wajen kawo ruɗu a ƙasarku Nijeriya). Ya Ra'is ka sani basu masauki da rashin yin katabus zai kawo illata. ( Waɗannan ƙasashen da aka kawo a hasashen nan sune ƙasashen da suke da dangantaka da rundunar Sufiyaniyawa, Ƙasashe biyu ne Saudiya da Isra'ila. Domin an ruwaici cewa rundunar Sufyaniy runduna ce ta Yahudu da larabawa.) Ku sanar da Alƙalin cewa; abubuwan da suka faru suka kuma wuce (na cutarwa, zubar da jini, rushe-rushe da yin maguɗin zaɓe) suna da tasiri  mai yawa wajen kawo gyara. Yana da muhimmanci ga alƙalin da ya  shigo cikin lamarin. Yanayi ne mai muhimmanci domin yin dukkan abin da ya dace nayin aiki mai farashi, domin shine  mutum ɗaya rak  da  zai iya magance komai na matsaloli a ƙasar. Allah ne masani akan komai, namu hasashe ne daga ɗan abin da muka sani, zartarwa na Ubangiji ne, domin shi mai yawan ilimi da hikima ne. Sai Malam Huda ya ɗaga hannu yayi addu'u nima na ɗaga tare dashi kamar haka: Ya Allah ka gaggauta nuna mana wannan lokacin da wannan alƙalin zai yanke wa ƙasarmu da al'ummarta hukunci na adalci, domin kawo gyara da warwarewa matsalolin da suka addabi wannan ƙasar tamu mai albarka. Ya Allah ka bashi dukkan taimako da kulawarka a gareshi, ka baiwa al'ummarmu dama da ikon karɓar hukuncin da zai yanke akansu da ƙasar gabaki ɗaya. Ka sanar da masu son ganin anyi adalci a ƙasarmu Nijeriya mai albarka, musulmai da kirista, harma da wanɗan da basu bin wani addini, su shirya domin an kusa nemansu zuwa ga muhimmin aiki. Allah kataimaki duk wani mai son ganin anyi adalci, ka basu juriya akan ganin tabbatara haka. Muhammad Sani Ra'is, Funtua. +2347034595991 03121440 04082019
http://isiyasy.blogspot.com/2019/08/baza-iya-kaucewa-zanga-zangar-juyin.html
0 notes